Abubakar Abba">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASUWANCI

Ba Da Mugun Nufi Shugaba Buhari Ya Garkame Iyakoki Ba – Ministar Kudi

by Abubakar Abba
October 24, 2019
in KASUWANCI, LABARAI, MANYAN LABARAI
2 min read
A Na Cigaba Da Zaman Doya Da Man Ja Tsakanin Majalisa Da Shugaba Trump
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ministar kudi da tsaretsare, Uwargida Zainab Ahmed Shamsuna, ta sanar da cewa, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nuna kun aincewa da rufe iyakokin Nijeriya da makwabtanta saboda ya na sane da matsanancin halin da tattalin arzikin kasashen zai shiga, inda ta kara da cewa, tunda farko bai amince da matakin ba, don haka ba da mugun a karshe ya amince da hakan ba.
Zainab Ahmad ta sanar da hakan a ranar Lahadin da ta wuce a yayin da ta ke ganawa da manema labarai a babban birnin Washington DC da ke kasar Amurka, inda ministar ta ce an dauki matakin ne don gyara alakar Nijeriya da makwabtanta. A cewar Hajiya Zainab, bankin bayar da lamuni na duniya, IMF na goyon bayan wannan mataki, saboda ya na sane da cewa ba wai an dauki matakin ba ne da nufin kuntata wa kasashen, sai dai kawai domin yin gyara ne ga tsarin alakar kasuwanci tsakanin kasashen.
Ta bayyana cewa, an yi ta kokarin daidaitawa da sauran qasashen, amma hakan ya faskara.
“Mun san akwai matsi ga tattalin arzikin qasashensu, saboda wannan  mataki, amma abinda mu ke so qasashen nan su gane shi ne cewa za su iya turo ma na kayayyaki, amma fa sai ta tashoshin jiragen ruwanmu,” in ji ta.
Ta jaddada cewa, dole ne kayan su shigo Nijeriya cikin sunduqai domin bai wa hukumar kwastom ta qasar damar bincikar su, sa’annan kuma su dinga biyan duk harajin da ya kamata, amma ba abinda su ke yi ba kenan, inda ta qara da cewa, “sai su bari a buxe sunduqai a qasashensu, sa’annan a shigo da kayan zuwa qasar nan ta varauniyar hanya.”
Ministar ta ce, Nijeriya ba za ta buxe iyakokinta ba har sai qasashen sun amince da bin tsarin cinikayya da kasuwanci na qungiyar qasashen yammacin Afirka, sa’annan ta qara da cewa har yanzu a na cigaba da tattaunawa a kan hakan.

SendShareTweetShare
Previous Post

Messi Ya Tseratar Da Barcelona A Wasan Su Da Slavia

Next Post

An Sanya Ranar Buga Wasan El-Classico

RelatedPosts

Da Dimi-diminsa: Buhari Ya Sauya Shugabannin Rundunonin Tsaro

Da Dimi-diminsa: Buhari Ya Sauya Shugabannin Rundunonin Tsaro

by Abubakar Abba
6 hours ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da murabus din shugabannin...

Zakzaky

Korona: Ku Mika Matar Sheikh El-Zakzaky Cibiyar Killacewa

by Abubakar Abba
14 hours ago
0

–Umarnin Kotu Ga Gidan Yarin Kaduna Daga Rabiu Ali Indabawa,...

Man Fetur

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

by Abubakar Abba
14 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan...

Next Post
An Sanya Ranar Buga Wasan El-Classico

An Sanya Ranar Buga Wasan El-Classico

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version