Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Ba Hannuna A Yunkurin Tsige Babban Jojin Ondo, Inji Malami

by Sulaiman Ibrahim
March 15, 2021
in LABARAI
2 min read
Malami
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya

Antoni Janar (AGF) kuma Ministan Shari’a a Nijeriya, Justice Abubakar Malami, ya yi fatali da ikirarin Babbar Alkalin jihar Ondo (CJ), Alkali Oluwatoyin Akeredole, da ta ce yana aikin hadaka da gwamnan jihar Rotimi Akeredolu da wasu domin ganin an cireta daga ofishinta.
Mai Shari’a Akeredolu ta yi zargin ne a wani karar da ta shigar a wani Babban kotun tarayya da ke Abuja inda ta shigar da gwamnan da wasu cikin kararta mai lamba FHC/ABJ/CS/2016/2021.
Wadanda take kara sun hada da Ministan Shari’a, gwamnan Ondo, Antoni Janar na jihar Ondo, Majalisar Dokokin jihar Ondo da Shugaban ‘yan sandan kasa (IGP).
Mai Shari’a Akeredole ta yi zargin cewa da gwamnan jihar, Kwamishinan Shari’a na jihar Ondo da Majalisar jihar sun sha alwashin  aiwatar da shiryensu na tsigeta ne bisa dogaro da zargi da wani makusancinta Olupelumi Fagboyegun da ke zarginta (CJ) a wani bidiyon da aka yada a kafafen Sadarwar zamani da ke cewa an tsareshi shekaru uku bisa rashin jituwar da ya shafi kadarorin zuri’arsu.
Har-ila-yau, CJ din ta kuma zargi Ministan Shari’a da shiga cikin lamarin domin ganin an tsigeta duk kuwa da cewa ba haka doka ya tanadar a yi na bincikenta ba.
Ta na mai cewa dukkanin wadanda shigar kotun suna kokarin cireta daga ofishinta a matsayin Babbar Alkalin jihar Ondo ta haramtacciyar hanya, don haka ne ta zo kotu domin dakatar da su daga daukan kowace irin mataki har sai an kammala sauran Shari’ar da ta shigar.
Sai dai a martanin da ofishin Ministan Shari’a ya fitar, ya sanya kafa ya shure zarge-zargen CJ din Ondo bisa cewa babu kamshin gaskiya kan batun.
A bisa haka ne ofishin nasa ya roki kotun da ta yi matsi da bukatar mai shigar da karar.
Alkaleri kotun tarayyar Justice Inyang Ekwo ya umarci gwamnan Ondo da sauran wadanda ake kara da su dakatar da daukan kowace irin mataki har zuwa sauraran kowace bangare.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sai Mun Tabbatar Kowane Kamfani Ya Fitar Da Gurabun Aikin Jama’ar Kumbotso – Kwamred Sabo

Next Post

Ambaliya: Kungiyar KDF Ta Raba Hatsin Naira Miliyan Biyu A Kebbi

RelatedPosts

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnatin Jihar Gombe ta sanar dokar...

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

by Daurawa Daurawa
14 hours ago
0

Daga Rabi'u Ali Indabawa, Abuja Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya,...

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

by Muhammad
18 hours ago
0

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira...

Next Post
Ambaliya: Kungiyar KDF Ta Raba Hatsin Naira Miliyan Biyu A Kebbi

Ambaliya: Kungiyar KDF Ta Raba Hatsin Naira Miliyan Biyu A Kebbi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version