Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

An Ba Jama’a Tabbacin Ganin Canji Kafin 2019

by Tayo Adelaja
September 20, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Awwal Umar, Minna

An bada tabbacin kafin cikar wa’adin mulkin nan na Shugaban Kasa Muhammadu Buhari jama’ar Nijeriya za su tabbatar da canjin nan da suka zaba. Mataimakin Sakataren jam’iyyar APC ta jihar Neja, Alhaji Audu Ibrahim ne ya bada tabbacin hakan a sakatariyar jam’iyyar lokacin da yake zantawa da manema labarai.

Alhaji Audun ya ci gaba da cewa ko a jiharsa ya tsaya ya na da abin nunawa jama’a musamman kan tsaro da ayyukan da suka shafi talakawa, domin kusan dukkanin karkarun jihar babu inda gwamna bai taba ba, musamman samar da wadataccen tubalin tsarin ilimin kimiyya da hanyoyi da kuma tsarin kiwon lafiya a jihar.

“A lokutan baya, muna kokawa akan matsin tattalin arziki da yayi mana dabaibayi, Allah cikin ikonsa da mai girma Shugaban Kasa ya tashi tsaye akan noma da hako ma’adinan kasa kowa ya ga inda aka dosa yanzu, ina da tabbacin jam’iyya za ta yi tsayin daka akan gwamnoni da shugabannin kananan hukumomi wajen ganin an ci gaba da bullo da hanyoyin da zasu amfani talaka.

“Tafiyar APC ba kamar tafiyar gwamnatocin baya ba ne, inda jama’a kan yi ruf da ciki da dukiyar jama’a a kyale su, mu kan a tafiyarmu babu raba in raba da dukiyar jama’a shi yasa muka tabbatar da cewar idanun jama’a ya bude wajen sanya ido akan duk wani abu da zai shigo aljihun gwamnati da yadda za a kashe shi, don haka duk wanda aka samu da kunbiya-kunbiya da kudin jama’a lallai jam’iyya za tai tsayin daka wajen ganin an fito da shi a hukunta shi.

“Ina da tabbacin wannan sabon zubin na shugabancin kananan hukumomi (ALGON) ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen goya ma duk shugaban karamar hukumar da aka samu da kokarin awon gaba da dukiyar Jama’a, lallai za su tabbatar da duk hanyoyin da za a bi wajen hukunta shi an yi hakan. Dan haka ina kira da babban murya akan shugabannin kananan hukumomi da su kara zage damtse wajen ganin jam’iyyar nan ta APC ta ba mara da kunya, domin dukkanmu amana ne ga jama’a kuma zamu tabbatar mun bi kowacce hanya wajen kare amanar dukiyar jama’a.”In ji shi

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Jami’an Tsaro A Jihar Nasarawa Sun Gargadi Masu Yada Jita-Jita

Next Post

Taimakon Al’umma Shi Ne Babban Burina –Hambali Shiitu

RelatedPosts

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Hussaini Yero, Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rahotan...

Mota

Yaki Da ‘Yan Ta’adda: Zulum Ya Ba Sojoji Gudummuwar Mota 12

by Muhammad
1 day ago
0

Sheran jiya Juma’a ce gwamna jihar Borno Babagana Zulum, ya...

Tsangaya

Yadda Aka Fara Karatun Tsangaya A Musulunci Da Lalacewarsa A Kasar Hausa – Gwani Yahuza 

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Shugaban hukumar kula da makarantun Al’kur’ani...

Next Post

Taimakon Al’umma Shi Ne Babban Burina –Hambali Shiitu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version