Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Ba Mu Amince Da Damka Wa Jihohi Ikon Mafi Karancin Albashi Ba – NLC Kebbi

Sai Mun Tuntube Ku Lokacin Duba Dokar – Majalisar Kebbi

by Sulaiman Ibrahim
March 11, 2021
in LABARAI
2 min read
Noman Damina: Gwamnatin Kebbi Ta Kaddamar Da Kwamitin Taki
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin-Kebbi

 

Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC) reshin Jihar Kebbi a jiya ta gudanar da zanga-zangar lumana, don nuna rashin amincewarta ga yunkurin cire  tsarin biyan mafi karancin albashin ma’aikata daga cikin Kundin Dokokin Nijeriya da wani dan Majalisar Dokokin Tarayya, Hon. Garba Datti, ya ke neman mambobbin majalisar su amince da kudirin, don bai wa jihohin kasar damar kayyade albashinsu.

Kungiyoyin ta Kebbi sun fito ne, domin yin tattaki a kafa tun daga bakin babban ofishin kungiyar Kwadago ta Jihar dake a kan titin tsohon gidan waya, wato NITEL, a cikin Babban Birnin Jihar, Birnin Kebbi har zuwa bakin harabar Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, wanda ya kai kimanin tafiyar kilomita uku, don kawai bayyana wa mambobbin majalisar rashin amincewarsu ga irin yunkurin da Majalisar Dokoki ta Tarayya ta soma gabatarwa.

Bisa ga hakan ne shuwagabannin Kungiyar Kwadago da sauran na wasu kungiyoyin suke nuna rashin amincewarsu ta hanyar gudanar da zanga-zangar lumana da kuma bada takarda a rubuce ga Majalisar Jihar.

Haka zalika, sun kara bayyana cewa, ya zama wajibi ga Majalisar Dokoki ta Jihar ta amince da bai wa bangaren gidan shari’a cin gashin kanta, sai kuma su tabbatar da sun shigo, don magance matsalar hauhawar farashin man fetur, musamman a Jihar Kebbi inda manoma ke yawan amfani da man fetur wurin ban-ruwan amfanin gona da suke nomawa.

Shugaban NLC na Jihar ,Kebbi Umar Haladu Alhassan, nan take ya isar da sakon uwar kungiyar ta kasa ga majalisar jihar.

A nashi jawabi, Kakakin Majalisar Dokoki na Jihar Kebbi, Rt. Hon. Samaila Abdulmuminu Kamba, wanda mataimakinsa Muhammad Buhari Aliero ya wakilta yayin karbar tawagar, ya ce, “muna ba ku tabbacin cewa, wannan yunkurin daga Majalisar Dokoki ta kasa yake, ba za a taba zartar da shi ba tare da amincewar  Majalisun Dokokin Jahohi 36 na kasar nan ba.

“Sobada haka idan aka aiko wa Majalisar Dokoki ta Jihar Kebbi, ba za mu  kaddamar da ita ba har sai mun kira taron masu ruwa da tsaki, don jin ra’ayinku. Haka kuma za mu duba sauran bukatunku, don yi musu adalci. Ina ba ku hakuri kan rashin halartar Kakakin Majalisar, wanda sa’anin aiki ne ya hana shi ganawa da ku.”

Ya kuma yaba wa shuwagabannin wadannan kungiyoyin da suka shirya wannan zanga-zangar ta lumana, don bayyana koken su ba tare da wata matsala ko hatsaniya ba.

Daga karshe kuma Mataimakin Kakakin ya gode wa dukkan mambobbin kungiyoyin kan hada kansu wuri daya, don tabbatar da cewa, wakilan da suka zaba sun yi musu wakilci mai ingance. Ya kuma kara da jan kunnuwansu  ga tabbatar da cewa, ba a samu wata hatsaniya ba.

SendShareTweetShare
Previous Post

Rigakafin Korona: Mun Amshi Allurai 59,280 A Adamawa – Shugaban Kwamitin

Next Post

Za Mu Fatattaki Bankuna Daga Maitama Makon Gobe, Cewar CBN

RelatedPosts

Malamai

Kungiyar Malamai Ta Tallafa Wa ‘Yan Hijira Sun Shirya Taron Bita Na Ramadan

by Muhammad
40 mins ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Kungiyar Hada Kan zauran Malamai da kungiyar...

Zakzaky

Ramadan: El-Zakzaky Ya Raba Tallafin Abinci Ga Mabukata

by Muhammad
45 mins ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Shugaban harkar musulunci a Nijeriya (IMN)...

Musulmi

Wajibi Ne Musulmi Su Ajiye Bambancin Akida Dan Hadin Kai Da Samun Zaman Lafiya – Shareef Ishak  

by Muhammad
50 mins ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, An bayyana cewar wajibi ne musulmi...

Next Post
Bankuna

Za Mu Fatattaki Bankuna Daga Maitama Makon Gobe, Cewar CBN

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version