Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Ba Mu Nada Muhammadu Sanusi Halifanci Ba –Darikar Tijjaniyyah

by Muhammad
March 15, 2021
in LABARAI
2 min read
Ba Mu Nada Muhammadu Sanusi Halifanci Ba –Darikar Tijjaniyyah
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar,

Shugaban darikar Tijjaniyya na duniya bakidaya, Sheikh Mahi Nyass ya musanta nada Mai Martaba tsohon Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II a matsayin shugaban Darikar a Nijeriya.

 

Nyass wanda shine dan Shehu Ibrahim Nyass, jagoran jaddada darikar Tijjaniyya ya bayyana hakan a tattaunawarsa da manema labarai a Sakkwato a ranar Litinin.

 

Ya ce nada Khalifan Darikar Tijjaniyya a Nijeriya da Afrika lamari ne na gabatar da wadanda ke bukata da tantancewa daga manyan Malamai a Nijeriya da Senegal.

 

“Ba a riga an tattauna wannan matsayar ba a kowanne irin waje, sai an cimma matsaya kafin a bayar da sanarwa. Bayan gabatar da sunan wanda ke nema daga shugabanni wajibi ne a gabatar da, takardar gabatarwa daga rukunin Malamai wadda babban jagoran Tijjaniyya na duniya ya sanyawa hannu kafin nada mutum wannan matsayin.” Nyass ya bayyana.

 

Ya ce a yanayin da ake ciki a yanzu, tsohon Sarkin Kano, Mai Martaba Sanusi II bai bi wadannan hanyoyin ba, kuma a kashin kansa bai gabatar da kansa ko ya nuna ra’ayin bukatar a nada shi shugabancin Darikar Tijjaniyya na Afrika ba.

 

Bugu da kari a wata tattaunawa ta daban da manema labarai, Sheik Ibrahim Dahiru- Bauchi, dan fitaccen malamin Addini, Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya bayyana yaduwar labarin nada Muhammad Sanusi II a matsayin shugaban Darikar a Nijeriya a matsayin labarin shaci fadi kawai.

 

Ya ce Darikar Tijjaniyya ta ginu ne a kan ilimi da koyarwar malamai da bin ka’idoji da tsare dokokin Allah. A cewarsa ba a fahimci bayanin da kanen jagoran Tijjaniyya Sheikh Makey ya yi ba a inda ya nuna Sarki Sanusi II ya tako sawun Kakansa, tsohon Sarkin Kano Muhammadu Sanusi I.

Ya jaddada cewar Makiy Nyass ya bayyyana yanayin al’amurran rayuwa kwatankwacin yadda aka cire Sarki Sanusi I a kan mulki shi ma Jikansa Sarki Sanusi II ya fuskaci irin wannan kaddarar a rayuwa.

SendShareTweetShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Malaman Firamire Da Dalibansu A Kaduna

Next Post

Tawagar Hadin Gwiwa Ta WHO Da Sin Ta Ba Da Shawarar Cigaba Da Binciken Asalin Annobar COVID-19 A Fadin Duniya

RelatedPosts

Malamai

Kungiyar Malamai Ta Tallafa Wa ‘Yan Hijira Sun Shirya Taron Bita Na Ramadan

by Muhammad
1 hour ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Kungiyar Hada Kan zauran Malamai da kungiyar...

Zakzaky

Ramadan: El-Zakzaky Ya Raba Tallafin Abinci Ga Mabukata

by Muhammad
1 hour ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Shugaban harkar musulunci a Nijeriya (IMN)...

Musulmi

Wajibi Ne Musulmi Su Ajiye Bambancin Akida Dan Hadin Kai Da Samun Zaman Lafiya – Shareef Ishak  

by Muhammad
1 hour ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, An bayyana cewar wajibi ne musulmi...

Next Post
Tawagar Hadin Gwiwa Ta WHO Da Sin Ta Ba Da Shawarar Cigaba Da Binciken Asalin Annobar COVID-19 A Fadin Duniya

Tawagar Hadin Gwiwa Ta WHO Da Sin Ta Ba Da Shawarar Cigaba Da Binciken Asalin Annobar COVID-19 A Fadin Duniya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version