Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home MANYAN LABARAI

Ba Na Tsoron Buhari Ya Kore Ni Daga Aiki – Ministar Mata

by Tayo Adelaja
September 6, 2017
in MANYAN LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tsohuwar ‘yar takarar Gwamnan Jihar Taraba, kuma Ministar Mata a Gwamnatin Muhammadu Buhari, Hajiya Aisha Jummai Alhassan ta ce a shirya take ta marawa tsohon mataimakin Shugaban Kasa, Alhaji Atiku Abubakar baya matukar ya tsaya takara a zaben 2019.

Ta ce sam ba ta tsoron ajiye aikinta na yanzu matukar bukatar hakan ta taso, domin ta dogara da Allah wanda yake bada mulki a lokacin da ya so.

A hirarta da sashen Hausa na BBC, Hajiya Aisha ta ce ‘yan adawa ne ke yi wa furucinta mummunar fahimta. A cewarta, da ma can ita tana goyon bayan muradun Atiku Abubakar, kasancewarsa ubangidanta, saboda haka ba ta ga dalilin da za ta juya masa baya ba.

Ta ce, koda Buhari zai tsaya takara a 2019, duk da cewa har yanzu bai nuna sha’awarsa ba, kuma shi ma Atikun bai ce mata zai tsaya ba, amma matukar su biyun za su tsaya, to za ta goyi bayan Atiku.

‘’Idan yanzu Buhari ya ce zai tsaya takara, koda ina matsayin Minista, zan je in durkusa gaban Baba Buhari in yi masa godiya. Domin ko shi kansa ba zai zarge ni ba, tun da ya san yadda muke da Atiku. Idan ma ya ga na juyawa Atiku baya ma, ina tunanin zai ce lallai ban kyauta ba, zai ce na ci amanar ubangidana.

‘’Ina girmama Muhammadu Buhari a matsayinsa na Shugaban Kasa, kuma zan ci gaba da girmama shi a har karshen rayuwata, kasancewar mutumin kirki ne da ya san ya kamata.’’

SendShareTweetShare
Previous Post

Amai Da Gudawa Ya Kashe Sama Da Mutum 20 A Kebbi

Next Post

Abinda Aka Yi Wa ‘Yan Kwankwasiyya A Kano Alamun Nasara Ne – Nasir Isah

RelatedPosts

Sufeton

Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Sufeton ‘Yan Sanda

by Muhammad
4 days ago
0

Waiwaye Game Da Manyan Sufetocin Da Aka Taba Nadawa A...

Malaman

Yajin Aiki: Malaman Jami’o’i Sun Ratse, Na Kwalejojin Fasaha Sun Tsunduma  

by Muhammad
4 days ago
0

Malaman jami’o’i a karkashin kungiyarsu ta ASUU sun ratse daga...

Gada

Gina Gadojin Sama: Ko Gasa Gwamnonin Jihohin Arewa Ke Yi?  

by Muhammad
5 days ago
0

Ra’ayoyin Kanawa Game Da Gadar Buhari Me Ya Sa Tambuwal...

Next Post

Abinda Aka Yi Wa ‘Yan Kwankwasiyya A Kano Alamun Nasara Ne – Nasir Isah

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version