Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba - Daliban Arewa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za Mu Shiga Zanga-zangar Da Za A Yi Wa Tinubu Ba – Daliban Arewa

bySadiq
1 year ago
Daliban

Daliban Arewacin Najeriya sun janye daga shiga zanga-zangar gama-gari da ake shirin gudanarwa kan yunwa da tsadar rayuwa a kasar.

Daliban, karkashin gamayyar kungiyoyin dalibai masu kishin Arewa, sun sanar da janyewarsu ce ta wata wasika da Shugaban Majalisar Dattawa ta Kungiyar Daliban Jihar Kano ta Kasa (NAKS), Kwamred Jibrin Sani Bello.

  • Tinubu Ya Aike Wa Majalisa Takardar Neman Kara N6.2trn A Kasafin Kudin Bana
  • Shugaban Amurka, Joe Biden Ya Kamu Da Cutar Covid-19

Ya bayyana cewa sun yanke shawarar kaurace wa zanga-zangar ce saboda rashin sanin asalin wadanda suka shirya.

Kwamred Jibrin Sani Bello ya ce, “Shirye-shiryen zanga-zangar gama-garin sun riga sun yi nisa, amma bayan mun yi tuntuba da kuma zurfafa tunani, mun ga akwai buƙata daliban Najeriya sun kaurace wa zanga-zangar shiga ciki ta, da saboda rashin sanin wadanda suka shirya,” in ji shi.

Daliban sun bayyana cewa yawancin zanga-zangar da ake gudanarwa na kawo tsaiko ga harkokin karatunsu.

Sun bayyana cewa duk da yake matsalar tsadar rayuwa ta addabi ’yan Najeriya, akwai bukatar a yi hattara kada a kara tsananta lamarin ta hanyar zanga-zanga mara kyakkyawan tsari.

“Mun yard yunwa da tsadar rayuwa sun addabi ’yan Najeriya, amma duk da haka akwai bukatar a yi hattara da shiga zanga-zangar da ba a san asalinta ba, wadda kuma ba a san irin mummunan sakamakon sa za ta haifar ba,” in ji Kwamred.

Sun bayyana zargin an saye wadanda suka shirya, shi ya sa kungiyoyin suka yanke shawarar kauracewa.

Maimakon zanga-zangar muna kira da a fadada shirin ba da tallafin karatu ga dalibai (NELFIND) ta yadda za a rika daukar nauyin daliban da suka cancanta su yi karatu a cikin gida da kasashen waje.

Wani dalibi a Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina, Abdulrahman Mansir, ya ba da misali da wasu lokuta a baya inda zanga-zanga ta sa aka tsawaita zangon karatu da birkita jadawalin karatun dalibai.

“Dole mu tsara kanmu a matsayinmu na dalibai, saboda zanga-zanga na iya kawo cikas ga ci gaban iliminmu kuma ba zai magance matsalolin Najeriya ba.

“Za mu koma ga Allah Ya magance mana matsalolin kasarmu,” in ji Mansur.

Matasan a Nijeriya sun ta shirin fita zanga-zanga ta tsawon kwanaki 10, wadda za a fara a ranar 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

Ko Kun San Miliyan Nawa Gombe Ke Kashewa Don Tsaftace Jihar A Duk Wata?

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version