Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Layin Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ya Lalace Sau 7 A 2024

byKhalid Idris Doya
12 months ago
Wutar

Babban layin samar da wutar lantarki ga al’umma a Nijeriya wato ‘National Grid’ a daren ranar Litinin ya lalace, inda ya jefa al’ummar kasar cikin duhu na rashin wuta, bayan sake gyara shi na ‘yan dakika a ranar Talata, kasa da awa 24 nan ma ya sake lalacewa, hakan ya zama layin ya lalace sau 7 a cikin shekarar 2024. 

Kamfanonin rarraba wutar lantarki (DISCOS) su ne suka sanar da lalacewa babban layin samar da wutar lantarki a daren ranar Litinin.

  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin
  • Ɗaliban Kwalejin Kimiyya Ta Jega Sun Yi Zanga-Zanga Har Da Ƙone-Ƙone

Daya daga cikin kamfanonin ya shaida cewa babban layin lantarkin ya lalace zuwa 0.00GW wajajen karfe 6:30 na yammacin ranar Litinin.

Kamfanin raba wutar lantarki na Inugu (EEDC) ya shaida wa kwastomominsa cewa sakamakon lalacewar babban layin wutar dukkanin wadanda suke samun wuta ta hannunsa ba za su samu ba a daidai wannan lokacin.

“Saboda haka, kan wannan lamarin, dukkannin tashoshinmu na TCN ba su samun wuta ba, don haka ba za mu samu damar rabar da wuta ga kwastomominmu da suke jihohin Abiya, Anambra, Ebonyi, Inugu, da Imo ba.

“Muna zaman jiran karin haske da cikakken bayani kan lalacewar wutar da kuma batun dawowar wutar daga cibiyar kula da wutar ta kasa (NCC).”

Kazalika, ita ma kamfanin rarraba wutar lantarki ta Abuja (AEDC) ta ce, “Ya ku kwastomominmu masu daraja, ku dan yi hakuri an fuskanci katsewar wutar lantarki sakamakon akasin da aka samu daga babban layin wutar lantarki ta kasa da karfe 6:58 na daren ranar Litinin, wannan ya shafi rabar da wuta da muke yi a yankunan da suke samun wuta daga garemu.

“Muna masu bayar da tabbacin cewa muna aiki tukuru da masu ruwa da tsaki wajen ganin an gyara wuyar nan ba da jimawa ba da zarar komai ya daidaita daga babban layin wutar. Mun gode da fahimtarmu.”

Tuni dai hukumar da ke kula da wutar lantarki a Nijeriya ta bayar da tabbacin cewa an dukufa wajen gyara wutan ta yadda ba za a sake samun jinkiri ba. Sun bai wa jama’a hakuri bisa dan karamin katsewar wutar da aka samu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Yadda Gwamnonin PDP Suka Ceto Damagun Daga Kora

Yadda Gwamnonin PDP Suka Ceto Damagun Daga Kora

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version