Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home Arewa Ta Yamma

Babu Mai Darajar Malami A Doron Kasa – SKY 

by Muhammad
April 7, 2021
in Arewa Ta Yamma
2 min read
Malami
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mustapha Ibrahim,

Alhaji Kabiru Sani Kwangila Yakasai Kano, wanda aka fi sani da SKY ya bayyana cewa babu wani mutum a doron kasa da ya kai darajar Malami, domin malamai su ne aka ce magada Annabawa, kuma Annabawa babu wanda ya kai su a doron kasa, domin su ne suka zo da sako daga Allah na abishi a ji tsoronsa a kadaita shi da kuma dukkanin ibadu kamar Kalmar Shahada, Sallah, Azumi, Zakka, zuwa Hajji ga mai iko, da sauran bayanin sako na hani da mummuna da umarni da kyakkyawa. Wannan shi ne aikin shugaban Annabawa da ma sauran halittu, don haka wannan aiki shi ne da mallamai suke yi na koyar da addini da suran mu’amaloli na rayuwa.

SKY ya bayyana haka ne a lokacin bikin yaye daliban makarantar Darul Hijrah Islamiyya da ke unguwar Technical GRA Nassarwa da ke cikin Karmar Hukumar Nassarwa da ke Kano da kewaye, taron da aka gabatar a ranar Lahadin da ta gabata.

“ Har ila yau ya ce mukamin Gwamna, Sarki da sauran shugabanni na da girma da daraja kasancewar su shugabaninmu amma gwamna da sarki da suransu ba su kai daraja Malami ba, domin in ka yi ibada dai dai ko wata mu’amala ta rikon amana, da tsoran Allah da duk wani abin yabo malami ne ya koya ma wannan ce ta tabbabar da Malamai darajarsu ta fi ta kowa,” a cewar Sky.

Shi ma a Jawabin sa shugaban makarantar ta Darul Hijrah Islamiyya Malam Khidir Lawan Balarabe, ce cewa ya yi wannan sauka ta Alkur’ani da wadannan dalibai suka yi ita ce Sauka ta tara, Kuma an yi walimar sauka dalibai 19 ne, a wannan rana, inda aka yaye mata 11 maza 8. A karshe Malamin ya ya ba wa SKY kan dawainiya da taimako da yake ga wannan makaranta da sauran al’umma da sauran al’mura na addinin Musulunci a ko da yaushe.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gidauniyar Khadimiyya Ta Kebbi Ta Ba Da Tallafi Ga ‘Yan Kasuwan Katsina 

Next Post

Za Mu Yi Aiki Tukuru Don Kyautata Ci Gaban Masarautar Gaya – Injiniya Sulaiman

RelatedPosts

Albashi

Raguwar Kason Gwamnatin Tarayya Ya Hana Mu Biyan Albashi Mafi Karanci – Gwamnatin Kano

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa...

Kasuwan Katsina

Gobara: Ganduje Ya Bai Wa ‘Yan Kasuwan Katsina Taimakon Naira Miliyan 20

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga El-Zaharadeen Umar, Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya...

Fawa

 Sana’ar Fawa Gado Na Yi Ba Taka Haye Ba -Sarkin Fawan Danmagaji

by Muhammad
2 weeks ago
0

Wakilinm da ke Zariya ISA ABDULLAHI GIDAN ‘BAKKO, ya samu...

Next Post
Gaya

Za Mu Yi Aiki Tukuru Don Kyautata Ci Gaban Masarautar Gaya – Injiniya Sulaiman

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version