Badakala: Majalisar Wakilai Ta Bayar Da Umurnin Cafke Gwamnan CBN, Babban Akanta Na Kasa Da Sauransu 
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badakala: Majalisar Wakilai Ta Bayar Da Umurnin Cafke Gwamnan CBN, Babban Akanta Na Kasa Da Sauransu 

bySulaiman
2 years ago
CBN

Kwamitin majalisar wakilai mai kula da kararrakin jama’a ya bayar da umurnin sammacin kama gwamnan babban bankin Nijeriya, Olayemi Cardoso, kan kin gurfana a gabanta domin amsa tambayoyi kan harkokin man fetur.

Kwamitin ya kuma bayar da umurnin kama Akanta Janar na Tarayya, Oluwatoyin Madein da wasu mutane 17.

  • Kisan Masu Mauludi A Kaduna Abun Takaici Ne – Bukola Saraki
  • ‘Yansandan Sun Kama Masu Laifi 130 A Watan Nuwamba A Katsina

Daga cikin mutane 17 da za a yi sammaci har da shugabannin Hukumar Kula da Zuba Jari ta Man Fetur (NAPIMS), kamfanin Ethiop Eastern Exploration and Production Company Ltd, da Western Africa Exploration and Production.

Sauran su ne, shugabannin Alteo Eastern E&P Co. Ltd., First Exploration & Production Ltd., The Md, First E&P Oml 8385 Jv, Heirs Holdings Oil da Mobil Producing Nigeria Unlimited (Mpnu).

Acikin jerin kamfanonin akwai manyan kamfanonin hakar danyen man fetur, Shell Petroleum Development Company (SPDC), Total Exploration & Producing Nig (TEPN), Nigeria Agip Oil Company (NAOC), Pan Ocean Oil Nig, Ltd, Newcross E&P Ltd da Frontier Oil Ltd.

An cimma matsayar ne a zaman binciken kwamitin domin duba karar da wani Fidelis Uzowanem ya shigar a ranar Talata.

Shugaban kwamitin majalisar, Hon. Michael Etaba (APC, Cross River), ya ce Cardoso da sauran wadanda ake tuhuma sun ki mutunta gayyatar da kwamitin majalisar ya yi musu.

Saboda haka, wani mamba a kwamitin, Fred Agbedi (PDP, Bayelsa), ya gabatar da bukatar bayar da sammacin kama duk wadanda sukaki mutunta gayyatar kwamitin.

Abedi ya ce, yana bukatar a gabatar masa da wadanda sukaki amsa gayyatar a gaban kwamitin a ranar 14 ga watan Disamba.

Kwamitin ya amince da kudirin, inda ya umarci Sufeto Janar na ‘yansanda, Kayode Egbetokun, da ya tabbatar an sammaci duk wadanda aka bayar da umurnin cafke su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Kasar Sin Za Ta Soke Harajin Kwastam Da Ta Buga Kan Kaso 98% Na Hajojin Wasu Kasashen Afirka 6

Kasar Sin Za Ta Soke Harajin Kwastam Da Ta Buga Kan Kaso 98% Na Hajojin Wasu Kasashen Afirka 6

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version