Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai

...Ta Nemi Karin Kasafin Kuɗi Ga Ma’aikatar yada labarai da wayar da kai

bySulaiman
9 months ago
Minista

Majalisar Dattawa ta yaba wa Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, bisa ƙoƙarinsa wajen gudanarwa da yaɗa bayanai kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati.  

 

An yi masa wannan yabon ne a ranar Talata yayin da ya bayyana a gaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yaɗa Labarai don kare kasafin kuɗin ma’aikatarsa na shekarar 2025.

  • Arsenal Ta Matsawa Liverpool Ƙaimi Bayan Doke Tottenham A Emirates 
  • Karkashin BRI Sin Ta Yi Hadin Gwiwar Samar Da Dakunan Gwaje-gwaje Sama Da 70

Sanatocin sun jinjina wa ƙoƙarin ma’aikatar amma sun nuna damuwa kan ƙarancin kuɗaɗen da aka ware mata, suna masu cewa ba zai wadatar ba don aiwatar da aikin ta na yaɗa labarai kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati.

 

Sun buƙaci a samar da ƙarin kasafin kuɗi na musamman domin a ƙarfafa wa ma’aikatar gwiwa.

 

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP-Kogi) ta jaddada bambancin kasafin kuɗin ma’aikatar da na ƙasar Afirka ta Kudu, inda ta bayyana cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Afirka ta Kudu ta samu kimanin naira biliyan 409 don aiwatar da shirye-shiryen ta.

 

Ta ce Nijeriya, wadda ke da yawan al’umma fiye da waccan ƙasar, ya kamata ta ware ƙarin kuɗi don shirye-shiryen ta na yaɗa labarai.

 

Ta kuma jaddada muhimmancin wayar da kan al’umma, musamman matasa, da kuma yadda ministan da tawagar sa suke shirye don aiwatar da hakan idan aka ƙara masu kuɗi.

 

Shi kuwa Sanata Abdul Ningi (PDP-Bauchi) ya yaba wa ministan bisa ƙwarewar sa, jagorancin sa, da kuma cigaban da aka samu a hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar, musamman ta fuskar cigaba da aka samu a Hukumar Tlabijin ta Nijeriya (NTA).

 

A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin, Sanata Ken Eze (APC-Ebonyi), ya buƙaci ma’aikatar da ta ƙirƙiro hanyoyin samun kuɗaɗen shiga.

 

Ya kuma buƙaci a sake duba kasafin kuɗin, yana mai jaddada muhimmancin ɓangaren yaɗa labarai ga nasarar gwamnati.

 

Ya ce: “Ba za a iya yin abubuwa da yawa ba idan babu kuɗaɗen shiga, kuma bayanai suna da matuƙar muhimmanci: muna buƙatar ɓangaren ya jagoranci manufofi da shirye-shiryen gwamnati.

 

“Kasafin kuɗin da ke gaban mu ba abin alfahari ba ne, idan an yi la’akari da abin da ake yi a wasu ƙasashe.

 

“Dole ne mu yi magana a matsayin ‘yan majalisa; dole ne mu ƙi amincewa da kasafin kuɗin ta hanyar kiran a ƙara yawan kasafin da aka ware wa ma’aikatar.

 

“Muna so Ministan Kasafi da Tsare-tsare na Ƙasa ya bayyana a gaban mu don sake duba kasafin kuɗin.”

 

A baya, ministan ya ƙiyasta cewa mafi ƙarancin adadin da ake buƙata don gudanar da ayyukan ma’aikatar yadda ya kamata ya kai naira biliyan 50.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version