Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home MAKALAR YAU

Bakon Marubuci: Tunasarwa Game Da Matsalar Daba A Siyasa (1)

by Tayo Adelaja
September 11, 2017
in MAKALAR YAU
5 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Dakta Sa’idu A. Dukawa

Yau kimanin shekara uku kenan da na gabatar da makala a SAS, Kano, game da matsalar daba a siyasa. Abin da ya afku a hawan daushe na wannan shekara ta 2017, na daba tsakanin magoya bayan ‘yansiyasa biyu, ya nuna bukatar sake tunasarwa game da bukatar kauce wa wannan mummunar dabi’ar. Don haka zan dada lika wannan mukalar.

Kamar yadda wani Bawan Allah ya taba nusarwa, zan raba tunasarwar kashi biyu ko uku saboda sauki ga mai karatu:

 

Gabatarwa

Babbar matsala a siyasar Nijeriya ita ce ta daba da amfani da kayan maye da matasa suke yi.

Matasa su ne jigon siyasa a kowace al’umma a tarihin duniya; amman matasan Nijeriya sun sha bamban wajen irin rawar da suke taka wa a siyasar Nijeriya a dalilin daba da ta’ammali da kayan maye da suke yi.

Daba kalma ce da take bayyana wata irin halayya ta matasa wadda ke haifar da sakamako mummuna; daba tana bada hoto na gungun matasa, masu shan kayan maye kamar giya, ko ganyen wi-wi, ko kwaya, ko roche, ko Benylin, ko kashin kadangare, da makamantansu, masu daukar makami, suna farma wadanda ba su ji ba ba su gani ba, ko kuma su farma junansu, ko su farma wanda aka saka su su farmasa.

Idan ‘yandaba suka shiga harkar siyasa, ana kiransu ‘’yanbanga’’; an samu kalmar banga daga kalmar Ingilishi ta banguard, watau ‘yan gaba-dai-gaba-dai!

Ba a taba harkar siyasa ba sai da banguard, watau masu tsayiwar daka, na ko a mutu ko ayi rai sai manufa ta tabbata. Amman idan suka tasirantu da kayan maye, to sun zama ‘yandaba.

 

Daba A Siyasar Nijeriya

A siyasar Nijeriya, daga jamhuriyya ta biyu banguard din siyasa sun zamo ‘yanbanga ko ‘yandaba; kadan daga aikinsu sun hada da yi wa iyayen gidansu zagi duk inda za su; da yi wa jama’a tsawa ko kyara idan maigidansu ya taho; da cin zarafin abokin hamayyar ubangidansu na siyasa; da kowa ko harmagaza idan ubangidansu yana yin jawabi a wajen kamfen; da yin magudi ranar zabe domin amfanin ubangidansu na siyasa; irin wannan magudi kuwa ya hada da jefa masa kuri’ar bogi, da korar wanda aka san danhamayya ne daga wurin zabe don hana shi yin zaben, da sayen kuri’a don maigidansu, da aikata duk wani hali wanda zai sa dattijai da masu mutunci su kyamaci zuwa wajen zabe, da tada fada a duk mazabar da aka fahimci ubangida ba zai yi nasara ba, da fasa akwatin zaben da aka fahimci danhamayya ya tasamma yin nasara, ko sace wannan akwatun.

Idan an ci zabe, ‘yanbanga ko ‘yandaba sukan tare a ofisoshin iyayen gidansu don yin maula ta hanyar tare duk wani mai shiga ofis su roke shi kudi; sukan je kafafen yada labarai don yin maganganu na karya da na gaskiya don yabon ubangidansu ko bata abokin hamayyarsa, ko yin raddi ga batancin da aka yi masa, ko tallata shi, da makamantansu su ne, masu kiran kansu sojojin baka, koda yake su sun sha bamban da ‘yandaba; sun fi kusanci da banguard; akan yi amfani da ‘yandaba ma don halaka abokin hamayya; idan suka rasa kudin yin shaye-shaye su kan haura gidajen mutane su yi musu sata, wani sa’in ma har su yi fyade ko kisan kai.

‘Yandaba suna da suna daban-daban: ana kiransu ‘yanjagaliya a Kano da Jigawa, ‘yansara-suka a Bauchi, ‘yan ECOMOG a Borno, ‘yan kalare a Gombe, kauraye a Katsina, area boys a yammacin kasar nan; da makatansu;

Ko ba a fada ba, babu al’ummar da za ta amince da harkar daba a siyasa, ballantana al’ummar Musulmi wacce aka ce mata ‘’kuntum khaira ummatin ukhrijat linnasi…; [ku ne fiyayyun al’umma da aka fitar a bayan kasa: kun kasance kuna umarni da kyakkyawa kuna hani da mummunan aiki, kuma kun yi imani da Allah…]; Kur’an, 3:110.’’

Ko tsarin mulkin Nijeriya ya haramta daba a harkar siyasa a sashe na 227: ‘’[ba a yarda wata kungiya ta mallaki ko ta tanadi ‘yandaba ba, ko ta bada horo ko makami ga wani ba, ko wasu mutane domin yin amfani da su wajen gwada karfi ko tursasawa don neman biyan bukatar siyasa, hasali ma ba a yarda a bar gurbin zato na cewar an tanadi karen bana domin yin maganin zomon bana ba].’’

 

Matasa Da Harkar Siyasa

Kamar yadda muka fada da farko, siyasa a ko’ina sai da banguard’, wadanda a ko’ina matasa ne.

A kasarar Girka (Greece), wadanda suka haifi tsarin dimokaradiyya, matasa ne wadanda suka jagoranci tafiyar: Socrates da dalibinsa Plato sun jagoranci matasa a kan akidar zuhudu da tsayawa a kan ra’ayi (idealism); su da dalibansu sun yi kokarin cusa wannan ra’ayi a zukatan matasa da tsarin siyasa; suna ganin idan ba an gyara halayyar dan’adam ba babu abin da za a tsinana a siyansance; amman da Aristotle, babban dalibin Plato, da nasa daliban irinsu Thomas Hobbes da John Locke, da J.J. Rousseau da Hegel da Karl Mard sun karkata akalar samari ne wajen fifita abin duniya, ko ra’ayin gina kasa da samar da abinci da kayan alatu a matsayin a’ala a tafikantar da gwamnati da jama’a (materialism). Su suna ganin gina kasa za a yi sai ruhin dan’adam ya gyaru. Wannan ra’ayin shi ya canza siyasar Turai da Amurka zuwa yadda muka santa a yanzu kuma ya shafi tunanin wasu ‘yansiyasar Afirka da Nijeriya.

Masu ilimin falsafa, matasa, Musulmi su suka yi kokarin daidaito da samar da tsakatsakin ra’ayi tsakanin gyaran hali da gina kasa. ‘Yanfalsafa irin su Alkindi da  Alfarabi da  Alghazali da Ibn Rushd da Ibn Taymiyya, da Ibn Khaldun, da su Abdullahi bn Fodio, duk sun taka rawar gani wajen samar da matsakaicin tunani da ya kamata a tafiyar da tsarin gwamnati. A kurkusa kuma akwai irin su Maududi, da Sayyid Kutub, da makamantansu; duk wadannan suna nuni da cewar duk kokarin gyaran halinka idan ka bar jama’a a cikin talauci za a samu matsala, haka kuma duk kokarin gina kasar ka, idan mutane ba su da ingantacciyar tarbiyya nan ma kana da matsala; shi ya sa muke da bukatar wadanda suke da irin wannan ilimin su karbi ragamar gwamnati su kuma su gwada jagorancin al’umma ko a gane bambancin.

A Afirka tun zuwan Turawan mulkin mallaka, matasa sun yi gwagwarmaya a mataki daban-daban: da Blyden da Senghor sun sa wa matasa kishin al’adun Afirka; da Awolowo da Azikwe sun nemarwa matasa gurbi a gwamnatin ‘yanmulkin mallaka; da Nkurumah, da Fanon, da Cabral, da Sekou Toure sun koyawa matasa turjiya da daukar makami don fatattakar Turawa; da Aminu Kano, da Raji Abdallah, da Sa’adu Zungur sun koyawa matasa ‘’na ki’’! Duk wadannan matasa ne wadanda suka jagoranci wasu matasan!

A siyasar Nijeryia, duk ‘yansiyasar Jamhuriyya ta farko matasa ne: irin su Maitama Sule, su Shehu Shagari, su Muhammadu Ribado, su Augustus Adebayo, su Sam Mbadiwe, wadanda su aka fi jin amonsu a Majalisa; da faduwar jamhuriyyar farko, sojojin da suka karbe ragamar mulki duk matasa ne: irin su Yakubu Gowon, su Muhammadu Buhari, su Sani Bello, su Sani Sami, da sauransu wadanda duk ba su rufa shekara talatin ba kowannansu. A duk misalan da muka bayar babu inda harkar daba ta shiga balle ta yi kamari.

 

Banga Mai Amfani A Siyasa

A iya cewa banga ta banguard tana da amafani ko tasiri a siyasa, amman ba ta shan kayan maye ba ko cutar da wani: misali, sai da aka yi fito-na-fito da Kuraishawan Makkah sannan Musulunci ya samu wurin zama, kuma matasa ne gatan wannan jihadin; haka kuma sai da aka yi juyin juya hali a France da Russia kafin Turawa su kwaci kansu daga zaluncin sarakunansu, da taimakon banguard; sai da matasan Afirka suka koyi turjiya kala-kala sannan aka samu ‘yancin kai; da aka kashe su Sardauna, har an kama wata turba daban matasan Arewa suka kwato mu ta juyin mulki; amman babu daya daga cikin misalan da suka gabata da za a kwatanta da harkar daba!

 

Dakta Sa’idu Dukawa Malami ne a Jami’ar Bayero, da ke Kano, drahmadsaid@yahoo.com

08033225331 (TES Kawai )   ciroma14@yahoo.com

SendShareTweetShare
Previous Post

Nahiyar Turai: Jemima Layzell: Yarinyar Da Ta Kyautar Da Sassan Jikinta

Next Post

Kafin Na Zama Edita…

RelatedPosts

Talaka

Allah Sarki Talaka!

by Muhammad
2 days ago
0

Kai! gaskiya ana fama da wani abu wai shi kirkirarren...

Ramadan

Ramadan Kareem Alhajin Allah 

by Muhammad
3 days ago
0

Yau a kofar gidan Alhajin Allah zai kwankwasa kofa da...

Kayan Abinci

Kalubalen Hauhawar Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

by Muhammad
4 days ago
0

A bahasin da hukumar kididdiga ta Nijeriya (NBS) ta wallafa...

Next Post

Kafin Na Zama Edita...

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version