El-Zaharadeen Umar">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home SIYASA

Bala Abu Ga Sanata Mandiya: Babu Taimakon Da Ka Yi Wa ‘Yan Gudun Hijirar Faskari

by El-Zaharadeen Umar
June 25, 2020
in SIYASA
2 min read
Bala Abu Ga Sanata Mandiya: Babu Taimakon Da Ka Yi Wa ‘Yan Gudun Hijirar Faskari
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Mataimakin Shugaban jam’iyyar APC yankin Funtua a jihar Katsina, Alhaji Bala Abu Musawa ya bayyana cewa Sanata mai wakilitar yankin Funtua, Sanata Bello Mandiya ya yi watsi da ‘yan gudun Hijirar da ke Faskari suna neman gudunmawa.

Bala Abu Musawa yana wannan magana ne a dai dai lokacin da ‘yan gudun Hijira mutun 3,700 wanda yawaicin su mata ne da kananan yara ke neman taimako a wata firamari da ke Faskari

Rahotanni sun bayyana irin gudunmawar da gwamnatin jihar Katsina da kuma shuwagabanin kananan hukumomin da ‘yan siyasa da masu hannu da shuni suka bada domin tallafawa waxannan baynin Allah su samun saukin rayuwa

Sai dai mataimakin shugaban jam’iyyar na cewa ya kamata Sanata Mandiya ya dawo ya san halin da mutanen shi ke ciki, ya kuma tausaya masu da taimaka masu kamar yadda wanda ya gada Sanata Abu Ibrahim ke yi lokacin da yake rike da wannan matsayin.

Kazalika mutanen yankin Funtua sun bayyana takaicinsu tare da nadamar zaben da suka yi wa Sanata Bello Mandiya a shiyyar Funtua, wanda bincike ya tabbatar da cewa babu wani tallafi ko Jaje balanta na gudummuwa daga Sanata Bello Mandiya

Mazauna wajen sun bayyana yadda masu rike da mukaman siyasa na yankin ke taimaka masu, misali Alhaji Bashir Ruwan Godiya mai ba gwamnan Katsina shawara akan harkar ilmi mai zurfi da kwamishinnan muhalli da dan majalisar jiha mai wakiltar su dama uwa uba gwamnan na Katsina duk suna tallafawa halin da suke ciki.

Sai dai duk da wannan korafi na mutanen wannan yankin, yasa an tuntubi Sanata Bello Mandiya domin jin ba’asin sa gane da wannan korafi ta hanyar buga waya da aika sakon kar ta kwana a wayarsa, don jin ta bakinsa, sai dai kash ba a samu nasarar hakan ba. Haka kuma mun yi kokarin jin ko yana da masu tafiyar da harkokinsa shima shiru kaki ji kamar an tura Bello Mandiya Sanatan Yankin Funtua

SendShareTweetShare
Previous Post

Buhari Ya Raba Gardamar Jam’iyyar APC Da Goyon Bayan Giadom

Next Post

Yadda Tattauna Batun ‘Korona’ Ya Haifar Da Hatsarin Jirgin Sama A Pakistan

RelatedPosts

Jiga-jigan Jam’iyyar PDP Sun Ziyarci Goodluck Jonathan

Jiga-jigan Jam’iyyar PDP Sun Ziyarci Goodluck Jonathan

by El-Zaharadeen Umar
2 weeks ago
0

Kwamitin sulhu na musamman na Jam'iyyar PDP, karkashin jagorancin tsohon...

Har Yanzu Sakkwatawa Ba Su Fara Morar Dimukradiyya Karkashin Mulkin Tambuwal Ba – Umar Lili

Har Yanzu Sakkwatawa Ba Su Fara Morar Dimukradiyya Karkashin Mulkin Tambuwal Ba – Umar Lili

by El-Zaharadeen Umar
6 months ago
0

Shugaban kungiyar matasan jihar Sokoto kuma dan gwagwarmayar ganin an...

Wane Ne Hon. Mal Samaila Suleiman (Dujiman Zazzau)?

Wane Ne Hon. Mal Samaila Suleiman (Dujiman Zazzau)?

by El-Zaharadeen Umar
8 months ago
0

Hon. Malam Sama'ila Sulaiman (Dujiman Zazzau) an haifeshi ranar 03/02/1981,...

Next Post
Yadda Tattauna Batun ‘Korona’ Ya Haifar Da Hatsarin Jirgin Sama A Pakistan

Yadda Tattauna Batun 'Korona' Ya Haifar Da Hatsarin Jirgin Sama A Pakistan

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version