Mahdi M Muhammad">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Ban Yarda Da Nuna rashin Girmamawa Ga Majalisar Dokokin Kasa Ba – Buhari Ya Gargadi Keyamo

by Mahdi M Muhammad
July 18, 2020
in LABARAI
2 min read
Ban Yarda Da Nuna rashin Girmamawa Ga Majalisar Dokokin Kasa Ba – Buhari Ya Gargadi Keyamo
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce, ya kamata a kowane lokaci Ministoci, Hukumomi da dukkan Shugabannin sassan su dinga nuna girmamawa ga Majalisar Dokokin kasa, shugabanninta da mambobinta.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis din da ta gabata, lokacin da Shugaban Majalisar Dattijai, Ahmed Ibrahim Lawan da Shugaban Majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila suka kawo masa ziyara a Fadar sa da ke Abuja.

samndaads

Shugaban, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis ta hannun Mataimakin sa na musamman kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, ya sake jaddada matukar girmamawar da yake wa Majalisar Dokokin kasar.

Ya ci gaba da cewa, ba zai dauki rashin girmamawa daga gurin wani memban ofishin zartarwa ga majalisar ba. A yayin tattaunawar tasu, sun bayyana abubuwan da suka faru kwanan nan a Majalisar. Tattaunawar tasu wanda ya dauki kusan tsawan awa daya, domin sun tattauna akan batutuwan da suka shafi mahimmancin kasa musamman rawar da majalisar dokokin ke taka wa wajen tallafawa da inganta rayuwar mutanen Nijeriya.

A ranar 30 ga watan Yuni ne, Karamin Ministan a Ma’aikatar kwadago da samar da aikin yi, Festus Keyamo ya samu sabani da wakilan Majalisar tarayya, lokacin da ya bayyana a gaban kwamitocin hadin gwiwar Majalisar Dokoki ta kasa kan samar wa matasa 774,000 aikin yi a karkashin Shirin Ayyukan Jama’a na Musamman (SPW).

A wannan lokacin ne jayayya da fadan kalmomi masu zafi suka shiga tsakanin Ministan da ‘yan majalisar. Don haka ne, majalisar ta ba da sanarwar dakatar da shirin.

Amma bayan haka ne, Shugaba Buhari, a ranar Talata, ya bayyana cewa, ya ba Ministan goyon baya ta hanyar ba shi damar ci gaba da aikin, duk da dakatarwar da Majalisar ta yi.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Tsaro: Babban Sifeton ‘Yan Sanda Na Kasa Sun Yi Ganawar Sirri Da Gwamnan Zamfara

Next Post

Kaduna Zuwa Jos: Hanyar Da Ta Shekara 20 A Lalace

RelatedPosts

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

by Mahdi M Muhammad
10 hours ago
0

Daga Abba Ibrahim Gwale, Shugaban kasa Muhammad Buhari ya amince...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yau Za A Yi Karon Batta A Zaben Kananan Hukumomin Jihar Kano

by Mahdi M Muhammad
19 hours ago
0

 Jam’iyyu 11 ne za su fafata PDP Kwankwasiyya ta ce,...

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Mahdi M Muhammad
20 hours ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Next Post
Kaduna Zuwa Jos: Hanyar Da Ta Shekara 20 A Lalace

Kaduna Zuwa Jos: Hanyar Da Ta Shekara 20 A Lalace

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version