Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

A Bar Yayata Labarin Abin Da Ba A Ji An Gani Ba – Badamasi Saleh

by Tayo Adelaja
September 23, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga A.A Masagala Benin

A cikin wata hira da wakilinmu na Bennin a Jihar Edo ya yi da shugaban al’ummar Arewa mazuna Jihar Edo, Alhaji Badamasi Saleh, shugaban ya nuna godiyarsa da kuma jinjina ga rundunar soja ta kasa a kan kokarin da take yi na ganin kasarmu tana ci gaba da zama kasa guda al’umma daya, tare da jaddada kira ga ‘yan Arewa mazuna Kudoncin da su kwantar da hankalinsu su zauna lafiya tare da kusanta kansu ga gwamnati da shugabanninsu.

Alhaji Badamasi ya nuna bukatar da ke akwai na ’yan Arewa mazuna Kudu maso-gabas da su kasance cikin natsuwa kuma guje wa yayata labarin abin da bai faru ba  domin hukuma da kafafen yada labarai ne suke da hurumin bayar da labarin abin da kasa take ci.

Kazalika, ya ce abu ne mai muhimmanci ga shugabannin ‘yan Arewa su rika fahimtar da jama’arsu muhimmancin kusantar gwamnati tare da wanzar da zaman lafiya. Ta bakinsa,  “Ina bai wa jagororin al’umman Arewa na nan Kudonci da su rika shirya tarurrukan neman hadin kai da zaman lafiya, ina ganin idon ana haka za a iya warware kowace irin matsala domin da ‘yan Arewa da ‘yan Kudu duk ‘yan uwan juna muke.

Haka nan, ya yaba wa gwamnonin Kudu dongane da irin bayanan da suka na na Allah-wadai da yunkurin da wasu suka yi na nuna bijirewa gwamnatin kasa. Ya ci gaba da cewa, ya kamata suma sarakunan Igbo su mara wa gwamnoninsu baya tare da jan kunnen matasansu masu tayar da kayar baya.

A karshe, Alhaji Badamasi ya nunar cewa su shugabannin ‘yan Arewa mazauna Kudoncin kasar nan dawainiyarsu ce ci gaba da fadakarwa da kuma wayar da kan jama’arsu lokaci-lokaci domin cimma zaman lumana.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Labarin Zainab Da Mubarak (2)

Next Post

Sinadarin Rayuwa: Muhimmancin Ilmi Ga ’Ya’ya Mata (2)

RelatedPosts

Kayan Marmari

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Yi Gyara A Kan Tsarin Makarantun Islamiyya

by Sulaiman Ibrahim
12 hours ago
0

Daga Sagir Abubakar Katsina Majalissar zartarwa ta Jihar Katsina ta...

Korar Ma’aikata A Kaduna Ta Kara Jefa Jama’a Mawuyacin Hali – Isah Ashiru

Korar Ma’aikata A Kaduna Ta Kara Jefa Jama’a Mawuyacin Hali – Isah Ashiru

by Sulaiman Ibrahim
12 hours ago
0

Daga Abubakar Abba, Kaduna Dan takarar Gwamnan Jihar Kaduna karkashin...

Babandede Ya Yi Gargadi A Kan Daukan Aiki Na Bogi Da Sunan NIS

Sauye-sauye Masu Ma’ana A Sashen Fasfo Na Hukumar Shige Da Ficen Nijeriya

by Yahuzajere
2 days ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), karkashin...

Next Post

Sinadarin Rayuwa: Muhimmancin Ilmi Ga ’Ya’ya Mata (2)

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version