Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Barcelona Za Ta Tafka Kuskure Idan Ta Yi Shari’a Da Neymar – Rivaldo

by Abba Ibrahim Wada
November 23, 2020
in WASANNI
2 min read
Rivaldo
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A satin da ya gabata ne kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta ce za ta gurfanar da tsohon dan wasanta, Neymar, a gaban kotu, saboda abinda ta kira biyan sa kudaden da su ka wuce kima da su ka kai Dala miliyan 12 lokacin da ya ke buga wa kungiyar wasa.

Jaridar El Mundo da a ke wallafawa a kasar ta Spain ta ruwaito cewar, Neymar, wanda ya yi wasa wa kungiyar Barcelona tsakanin shekarar 2013 zuwa 2017, ya karbi kudaden da su ka wuce kima daga kungiyar a matsayin albashi.

samndaads

Rahotanni sun ce, dan wasan na Brazil na daga cikin sahun farko na ’yan wasan da su ka kauce wa biyan haraji a Spain, inda a ke bin sa bashin sama da Yuro miliyan 34.5, wanda hakan ta sa har hukumomin kasar su ka gurfanar da shi a gaban kotu.

Sai dai tsohon dan wasan kungiyar sannan tsohon dan tawagar Brazil, Rivaldo, ya bayyana cewa, babban abin kunya ne idan a ka ji kungiya mai girma kamar Barcelona ta na shari’a da tsohon dan wasanta, Neymar, a kotu.

Rivaldo ya ci gaba da cewa “Idan akwai wani abu tsakanin Barcelona da dan wasan yakamata su zauna su san abinda yakamata domin a warware matsalar sannan kuma har Neymar zai iya sake komawa kungiyar a nan gaba”

Daman dai hukumomin kasar Sipaniya suna gudanar da bincike akan lokacin da Neymar yaje Barcelona da kuma tafiyar sa PSG sannan wata Kotu a kasar ta bukaci Neymar da ya biya Barcelona yuro miliyan 6 da dubu 790,000.

Sai dai har yanzu dan wasan bai ce komai ba akan wadannan maganganu da akeyi a ya yinda yake ci gaba da jinyar ciwon daya samu a kafarsa kuma a kwanakin baya kungiyar ta PSG ta bayyana cewa zata karawa dan wasan sabuwar yarjejeniya.

A shekarun da suka gabata dai Barcelona taso ta sake sayan dan wasan daga PSG sai dai daga baya cinikin bai kasance ba sakamakon kudin da PSG ta bukata Barcelona ba zata iya biya ba kuma tun kafin bullar cutar Korona ma.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Rashin Messi A Gasar La liga Babbar Barazana Ce, Cewar Figo

Next Post

Yadda Mai Maganin Gargajiyar Ke Duba Marasa Lafiya Sama Da 200 A Jos Kullum

RelatedPosts

Klopp

Bai Kamata Mu Yi Rashin Nasara A Hannun Manchester Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
3 hours ago
0

Mai koyar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Liverpool,...

Arsenal

Har Yanzu Arsenal Tana Zuciyata – Ozil

by Abba Ibrahim Wada
5 hours ago
0

Tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa t arsenal, Mesut Ozil...

Za Mu Iya Samun Nasara Ba Tare Da Messi Ba – Koeman

by Abba Ibrahim Wada
5 hours ago
0

Duk da rashin Messi sakamakon horon dakatarwa na wasanni biyu...

Next Post
Marasa Lafiya

Yadda Mai Maganin Gargajiyar Ke Duba Marasa Lafiya Sama Da 200 A Jos Kullum

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version