Barista Aysha Ahmad: Gwarzuwar Tabbatar Da Adalci Da Dogaro Da Kai
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barista Aysha Ahmad: Gwarzuwar Tabbatar Da Adalci Da Dogaro Da Kai

byBilkisu Tijjani
2 years ago
Aysha

Barista Aysha Ahmad, kwararriyar lauya ce kuma mai ba da shawarwari ta fuskar Shari’a da harkokin rayuwa, wacce ta tsaya tsayin daka wajen kawo sauyi da karfafa samar da ayyukan dogaro da kai a garinta na haihuwa Zariya da ke Jihar Kaduna. Haifaffiyar garin Zariya ce, birni mai cike da tarihi da al’adu.

Ta yi karatu a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, inda ta samu digiri a fannin zama kwararriyar lauya (LLB). Daga nan ta samu nasarar shiga makarantar lauyoyi ta Nijeriya tare da cimma nasarori masu dimbin yawa a shekarar 2005.

  • Jarin Da Sin Ta Zuba A Bangaren Sufuri Ya Karu A Cikin Watanni 11 Na Farkon 2023
  • Amurka Ta Lalata Manufarta Ta Fadin Albarkacin Baki Wajen Watsa Labarai

A kokarinta na fadada neman kwarewa a fannin karatun shari’a, Barr Aysha Ahmad ta wuce zuwa kasar Ingila inda ta samu digirinta na biyu a fannin shari’a a Jami’ar Salford da ke kasar, inda ta karfafa iliminta tare da samun kwarewa a fannonin zamantakewar Duniya.

A daya bangaren kuma, Barr Aysha Ahmad ita ce shugaba kuma mamallakiyar Kamfanin Lauyoyi na Essence Chambers, kamfanin da ya kware wajen tsayawa da wakiltar ‘ya’ya mata da kananan yara Hausa/Fulani a kafatanin Garin Zariya a bangaren shari’a.

Aysha

Wannan ke kara jaddada sadaukarwarta don warware shinge da tufka da warwara a cikin aikin tabbatar da adalci.

Tasirinta bai tsaya a kotu kadai ba, domin yunkurin da ta yi na kawo sauyi a zamantakewa ya sa ta kafa gidauniyar kula da yara mata ta sarauniya wato (Sarauniya Girls Child Care Foundation).

Aysha
Wannan gidauniya ta zama hanyar jinkai da share hawaye ga masu karamin karfi a fadin birni da karkara a Nijeriya, ta hanyar samar da sabbin tsare-tsaren yaki da fatara gami da samar da Tallafi.

Aysha Ahmad ta sadaukar da kanta ga inganta rayuwar marasa galihu, musamman ‘yan mata, tare da samar da guraben ayyukan dogaro da kai ya sa ta samu matukar karbuwa sosai a tsakanin al’umma.

Aysha
Ta kasance mai yawan halartar tarukan kara wa juna sani da manyan tarukan al’umma wanda wannan ya kara haskaka kwarewarta a duniya.

Bayan dimbin yabo da take samu daga ba’arin mutane, ta zama abin koyi ga mutane da yawa masu burin ganin sun kwaikwayi ayyukanta na tausayin al’umma, har ma aka yi mata lakabi da Jagorar Tabbatar da Adalci da Ayyukan Jin kan Al’umma, wato ‘Icon of Justice & Humanitarian Serbices’, Saboda jajircewarta wajen tsayawa kan gaskiya, daidaito, da ci gaban al’umma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

August 31, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Next Post
Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

Sin Ta Yanke Shawarar Kakaba Takunkumi Ga Kamfanonin Tsaron Amurka Guda Biyar

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version