Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Baru Ya Mayar Wa Da Kachikwu Martani

by Tayo Adelaja
October 10, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga  Idris Aliyu Daudawa

Babban jami’in gudanarwa na Hukumar kula da albarkatun mai ta ƙasa NNPC, ya  fasa ƙwai akan zargin da ake mashi na, ƙin bin ƙa’idojin da aka shimfiɗa wajen bada kwangiloli.

Idan dai ba a manta ba makon da ya gabata ne, ƙaramin Ministan man fetur, Ibe Kachikwu ya rubuta wa shugaban ƙasa Muhammadu Buhari wata takarda, inda ya yi zargin Baru bai bi ƙa’idojin da aka shimfiɗa yadda ya dace wajen bada kwangiloli ba.

A wata doguwar takarda da aka fitar ranar Litinin ta hannu mai magana da yawun Hukumar albarkatun mai ta ƙasa, mai suna Ndu Ughamadu ya,kare wanda ake yi ma zargin ya ce shi zargin da ake bai da wata makama bare kuma ace tushe, bugu da ƙari kuma duk lokacin da za a bada wata kwangila, a na bin yadda doka ta ce a yi.

Maganar kwangilar da aka bada ta NPDC wannan an bi ƙa’ida, kazalika AKK  ita ma majalisar zartaswa ta ƙasa, ba a kai ga lokacin da za a bada kwangilar ba.

Ya ƙara da cewam da yake an buga yadda ake zargin ba a bi ƙa’ida ba, wajen bada kwangilolin NNPC a jaridu, sai shugaban ƙasa ya buƙaci babban jami’in gudanarwa na NNPC shi da ‘yan tawagarsa, da cewar su kare kansu, akan zarge-zargen da ake yi masu. Ita dai takardar da ƙaramin ministan mai ya miƙa a ranar 30 ga Agustar 2017, ta nuna cewa yawancin kwangilolin da aka bayar, ko kuma ba a sake fasalinsu ba, ba wanda ya taɓa tattaunawa da shi.

Babban abin da aka fi su kuma mai muhimmanci shi ne, tun daga farko, ba sai an sake fasalin kwangila ba, ko kuma a tattauna da ƙaramin minista, ko kuma su ɓangaren da ke amincewa da al’amuran da suka shafi kwangilar NNPC. Abu mai muhimmanci shi ne, shugaban ƙasa a matsayin shi na ministan albarkatun mai.

Da akwai wani lokaci da za a iya shiga wanda duk abin da ake so bai wuce amincewar mambobin ɓangaren bada kwangilar NNPC ba, Sai kuma ta wani ɓangaren, wannan kuma ya dace ne da yadda kwangilar ta ke, wannan ana buƙatar amincewrar shugaban ƙasa, kamar yadda ita wasiƙar kwangilar ta fayyace, ko kuma su majalisar zartarwa su amince da bada kwangila.

 

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

2019: PDP Ta Sha Alwashin Karɓe Kujerar Ganduje

Next Post

Haƙar Mai Da Harkar Tsaro: Buhari ya Gana Da Gwamnonin Arewa Uku

RelatedPosts

Allurar Rigakafin

An Fara Yin Allurar Riga-kafin Korona a Nijeriya

by Muhammad
7 hours ago
0

Yau Ake Sa Ran Buhari Da Osinbajo Za Su Karbi...

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
1 week ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Adaidaita

Yajin Aikin Adaidaita: Acaba Ta Dawo A Kano

by Muhammad
2 weeks ago
0

Ya Jefa Jama’a Cikin Tsaka Mai Wuya Yadda Aka Koma...

Next Post

Haƙar Mai Da Harkar Tsaro: Buhari ya Gana Da Gwamnonin Arewa Uku

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version