Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Batun Yajin Aiki Ba Gudu, Ba Ja Da Baya –ULC

by Tayo Adelaja
September 18, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sulaiman Bala Idris, Abuja

Kungiyar Kwadago ta ULC, wacce ta ke kishiyantar kungiyar NLC, za ta fada yajin aiki daga yau Litinin 18 ga Satumbar 2017, matukar ba an shawo kan wata yarjejeniya da aka cimma akan bukatun da tace ta gabatarwa gwamnati tun cikin watannin baya ba.

samndaads

Cikin kungiyoyin da suke a karkashin wannan kungiyar ta ULC har da NUPENG, masu dakon man fetur, da ma’aikatan wutar lantarki da bankuna da kuma matuka jiragen sama da na kasa da dai sauranasu.

Duk da gargadin da gwamnatin tarayya ta yiwa kungiyar kwadago ta ULC ‘United Labour Congress’, kungiyar ta ce babu wani barazana da zai yi musu tasiri har su janye yajin aikin da zasu fara a yau Litinin.

Ya ce, “Wannan yajin aiki, duk da ba kaunarsa muke ba, shi ne kadai matakin da zamu iya dauka. Mun yi iyaka kokarinmu wurin bin hanyoyin sulhu don magance matsalar, amma hakan bai yiwu ba.

“A dalilin haka muke kiran ‘yan kasa masu kishin kasa da su bamu hadin kai domin tunasar da gwamnatin tarayya da gwamnonin jihohi akan su yi adalci wurin sauke nauyin da ke rataye a wuyansu.”

Shi ma Sakataren tsare-tsare na kungiyar kwadago ta ULC, Kwamared Nasir Kabir, ya bayyanawa manema labarai cewa kadan daga matsalolinsu har da Ministan Kwadago, Dakta Ngige, wanda ya ce yana nuna son zuciya, ta wajen fifita kungiyar NLC, domin ya ki ya saki lasisin rijistar kungiyar ta ULC, da kuma rashin biyan ma’aikata albashinsu da gwamnonin jihohi suke yi.

A daya bangaren kuwa, yayin da yake sharhi kan illar yajin aiki ire-iren wannan ga tattalin arzikin kasa, shugaban sashen koyon ilmin tattalin arziki da dabarun kasuwanci a kwalejin kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, Dakta Lawal Habeeb Yahya, ya ce hakan zai sake mayar da hannun agogo baya, ga tattalin arzikin da yake kokarin tsamo kan shi daga koma bayan da ya shiga, shekaru biyu da suka wuce.

Sai dai ya zuwa hada wannan rahoton, duk wani kokari da wakilinmu yayi don jin matsayar ma’aikatar Kwadagon Nijeriya, abin ya ci tura.

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yar’adua Ya Kuduri Aniyar Rigima Da Ni, Ya Tsinci Kansa A Kabari –El-rufai

Next Post

BABBA DA JAKA

RelatedPosts

Zakzaky

Korona: Ku Mika Matar Sheikh El-Zakzaky Cibiyar Killacewa

by Muhammad
21 hours ago
0

–Umarnin Kotu Ga Gidan Yarin Kaduna Daga Rabiu Ali Indabawa,...

Rigakafi

Korona: Jiga-jigan Nijeriya Na Sulale Wa Waje Amsar Rigakafi

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Biyo bayan sake bullar annobar Korona...

Kawuna

Kawuna Ya Turo Ni Kano Don Yin Garkuwa Da Mutane, In Ji Maryam  

by Muhammad
5 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Maryam Muhammad, wadda ta shahara wajen...

Next Post

BABBA DA JAKA

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version