Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home KASASHEN WAJE

A Bi Zancen Koriya Ta Arewa Da Sannu -Putin

by Tayo Adelaja
September 12, 2017
in KASASHEN WAJE
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tare da Sani Anwar 08036365416 (leadershipayau.com)

Shugaban Amurka da takwaransa na kasar Koriya ta kudu na kiran a kara sanyawa koriya ta arewa takunkumi. kasashen China da Rasha, dake manyan kawayen Koriya ta arewa, sun ce kiraye-kirayen da ake yi na kara zafafa takunkumi akan Koriya ta arewa bayan gwajin makamin Nukiliyar da ta yi na baya-baya ba zai taimaka ba sosai wajen rage fargaban da ake fama da shi a mashigen koriyoyin biyu.

Da ya ke magana a wajen taron kolin kasashen Brazil, Rasha, da Indiya, da kuma China, na kasashe masu bunkasar tattalin arziki da ake yi a birnin Diamen na kasar China, shugaban Rasha Bladimir Putin yayi Allah Wadai da gwajin makami mai linzamin da Koriya ta arewa tayi na baya-baya, amma yayi gargadin cewa ruruta wutar daukan matakin soja zai iya haddasa bala’i a duniya.”

Putin ya kuma caccaki Amurka akan kiran da ta yi na a kara sanyawa Koriya ta Arewa takunkumi. Ya kira matakin “Mara amfani wanda kuma ba zai yi aiki ba”. Ya kara da cewa shashanci ne Amurka ta sanyawa Rasha takunkumi saboda tana kasuwanci da Koriya ta arewa, kuma daga baya ta dawo tana neman Rasha ta taimaka ta sanyawa yanken da aka maida saniyar ware takunkumi.

Kasashen Rasha da China, da ba sa goyon bayan sanyawa Koriya ta arewa takunkumi, sun roki Amurka da koriya ta kudu kwanan nan, su kawo karshen atisayen sojan da suke yi, don takawa Koriya ta arewa burki akan gwajin makamai masu linzami da na nukiliya da take yi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sanata Misau Ya Nuna Farin Cikinsa Ga Matakin Hukumar ‘Yan Sanda

Next Post

China Za Ta Goyi Bayan Matakin Kwamitin Sulhu Kan Koriya Ta Arewa

RelatedPosts

Mijin Sarauniya Elizabeth Ta Ingila Ya Mutu

Mijin Sarauniya Elizabeth Ta Ingila Ya Mutu

by Muhammad
4 days ago
0

Rahotanni daga Fadar Buckingham ta kasar Ingila sun tabbatar da...

Nijer

Matan Nijer Sun Dage Kan ‘Yancinsu Bayan Kotu Ta Sako Wasu Shugabanninsu

by Muhammad
4 weeks ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Hukumomi a jamhuriyar Nijer sun sako...

Magufuli

Muhimman Abubuwa Goma Game Da Tsohon Shugaban Tanzaniya John Magufuli

by Muhammad
4 weeks ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Al'ummar kasar Tanzania suna zaman makokin...

Next Post

China Za Ta Goyi Bayan Matakin Kwamitin Sulhu Kan Koriya Ta Arewa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version