Biden Ya Turo Tawaga Don Halartar Rantsar Da Tinubu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Biden Ya Turo Tawaga Don Halartar Rantsar Da Tinubu

byAbubakar Abba
2 years ago
Biden

Shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya bayyana tawagar kasar da za ta halarci rantsar da zabben shugaban kasa Asiwaju Bola Tinubu da za a yi a ranar 29 ga watan Mayun 2003.

An gayyato wasu shugabannin kasashen duniya, don halartar rantar da tsohon gwamnan Jihar Legas Tinubu a dadandalin Eagle Square da ke Abuja, inda Tinubu zai kasance shugaban kasa na 16.

  • An Kwashe Wa Juventus Maki 10 A Gasar Seria A
  • Kwana 6 Ga Rantsar Da Tinubu: ‘Yan Jarida Sun Yi Tsokaci Kan Yadda Aka Miƙa Mulki A Gwamnatocin Baya

Ana kuma sa ran tsoffin shugabanin kasa, jakadu da wakilan hukomomin gwamnati na kasa da kasa, za su halarci rantsuwar.

Biden, cikin sanarwar da fadar shugaban kasar Amurka ta wallafa a Intanet a daren jiya Litinin, ya sanar da sunayen tawagar Amurka ta mutum tara wadda sakataren Amurka na sashen gidaje da bunkasa birane Marcia L. Fudge zai jagoranta.

‘Yan tawagar na Amurka sun hada da, Mista David Greene, mai kula harkokin ofishin jakadancin Amurka a Nijeriya da ke Abuja, Hon. Sydney Kamlager-Dove, wakilin Amurka da ke a California, Hon Marisa Lago, sakataren harkokin kasuwanci na kasa da kasa, Janar Michael E. Langley, kwamandan Amurka na rundunar Amurka da ke aiki a Afrika, Hon Enoh T. Ebong, Daraktan hukumar sashen kasuwanci ta Amurka.

Sauran su ne, Hon Mary Catherine Phee, mataimakin sakataren Amurka na sashen harkokin Afrika, Hon Judd Devermont, mai taimaka wa shugaban kasa na musamman da kuma Hon Monde Muyangwa, mataimaki a sashen mulki na Amurka da ke aiki a Afrika.

A cikin shire-shiryen rantsar a rana 27 da watan Mayu, tsohon shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta, zai gabatar da kasida mai taken zurfafa demokiradiyya don a bunkasa.

Haka zalika, a ranar Alhamis, za a tabbatar wa Tinubu matsayin babban kwamandan tsaro na kasar nan GCON, inda kuma shugaban kasa mai barin Gado Muhammadu Buhari, zai karrama zababben mataimakin sa sanata Kashim Shettima, da lambar GCON.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Next Post
Na Rufe Iyakoki Ne Don Karfafa Guiwar ‘Yan Nijeriya – Buhari

Na Rufe Iyakoki Ne Don Karfafa Guiwar 'Yan Nijeriya - Buhari

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version