Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Bikin Ista: Saraki Ya Nemi Kirista Su Yi Koyi Da Ɗabi’ar Sadaukarwa

by Rabiu Ali Indabawa
April 4, 2021
in LABARAI
2 min read
Bikin Ista: Saraki Ya Nemi Kirista Su Yi Koyi Da Ɗabi’ar Sadaukarwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabi’u Ali Indabawa, Abuja

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Dr. Abubakar Bukola Saraki ya taya ɗaukacin Al’ummar Kiristan duniya, musamman ma na Nijeriya murnar bikin Ista; bikin dai yana alamta tunawa da zagayowar ranar da Almasihu ya farfaɗo ne.

A saƙon nasa, Dr. Saraki ya hori Kiristoci da su kwaikwayi ɗabi’ar sadaukarwa don hakan zai haifar da bunƙasa da ɗorewar Nijeriya.

Dr. Saraki ya bayyana hakan ne a wata sanarwar manema labarai da ofishin yaɗa labaransa ya fitar yau a Babban Birnin Tarayya, Abuja. Ya ce, bikin Ista na alamta sadaukarwar da Yesu Almasihu ya yi domin amfanuwar al’umma, kuma duk wanda ke biyayya da ɗa’a ga koyarwarsa dole ne ya yi koyi da halayensa nagartattu domin amfanin kasarsa da ma duniya baki-ɗaya.

Ya ƙara da cewa, a wannan lokaci da Nijeriya ke fuskantar matsalolin da suka shafi harkar tsaro, tattalin arziki da sauransu, dole ne ‘yan ƙasa su kasance na gari su kuma yi koyi da halayen kwarai na Almasihu don a samu a fice daga wannan halin da ake ciki.

“Ina kira ga ‘yan Nijeriya da su yi koyi da ɗabi’ar ƙaunar juna da kuma ƙaunar ƙasasarsu. Ina da tabbacin cewa idan muka yi hakan zai taimaka mana wurin magance matsalolin da ke neman tarwatsa mana ƙasa, kuma za a samu haɗin kai.

“Dole ne mu yi amfani da wannan dama wurin bayyana cewa dukkaninmu ‘yan Nijeriya ne kafin kasantuwarmu Kirista ko Musulmi. Duk ‘yan Nijeriya, ba tare da la’akari da abin da suke bauta wa ba, dole mu kasance masu tsoron Allah ba kawai mu riƙa amsa sunan masu addini ba.

“Ina ƙara taya ‘yan uwanmu Kirista murnar bikin ranar Ista ta shekarar 2021.” Inji Saraki

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Mu Tuna Da Shahidai Tare Da Shugaba Xi Jinping

Next Post

Anci Tarar Kungiyar Katsina United

RelatedPosts

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

Gwamnatin Gombe Ta Sanya Dokar Hana Fita A Garin Balanga

by Rabiu Ali Indabawa
12 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnatin Jihar Gombe ta sanar dokar...

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

Ramadan: Mu Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ga Nijeriya, Inji Bukola Saraki

by Rabiu Ali Indabawa
14 hours ago
0

Daga Rabi'u Ali Indabawa, Abuja Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya,...

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

Ramadana: Lokaci Ne Na Komawa Ga Allah, Inji Atiku

by Rabiu Ali Indabawa
18 hours ago
0

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira...

Next Post
Katsina United

Anci Tarar Kungiyar Katsina United

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version