Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

byLeadership Hausa
4 months ago
Muhalli

Duba da yadda Nijeriya ke ci gaba da fuskanatar kalubalen kula da kare muhalli, a nan za a iya cewa, zagayowar bikin ranar kula da muhalli ta duniya, ta zo kan gaba.

Taken taron na 2025, shi ne, yakar zubar da robobi, musaman da ake kira a turance,‘Take Way’ da ke haifar da gurbatar muhalli.

  • Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB

Zubar da wadannan robobin, na shafar kiwon lafiyar alumma da lalata ruwan da ke a cikin Koguna da kuma abincin da bil Adama ke ci.

Kazalika, zuba su da ake yi a cikin Kona, sukan yi ambaliya, su zuwa cikin gonakai da cikin birane, musaman duba da cewa, a daukacin fadin duniya, an mayar da hankali ne, wajen daukar matakan gaggawa domin kare muhalli.

Ministan Ma’aikatar Kula da Muhalli Balarabe Abbas Lawal, a jawabin da ya yin a bikin ranar ya jaddada bukatar daukar matakan gaggawa, kan gurbata muhalli, mussamman duba da cewa, kalubalen, na shafar lafiyar bil Adama.

Abbas ya kuma jaddada bukatar da dauki matakai, kan aukuwar sauyin yanayi, musamman duba da matsalar talauci da kuma ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro, da kasar nan, ke fuskanta.

Bugu da kari, Hukumar kula da ‘yan cirani ta duniya wato IOM ta sanar da cewa, gurbata muhalli da robobin da aka sarrafa zuke haifarwa, suna taka gudunmwa, wajen aukuwar dumamar yanayi da kuma gurbata muhalli.

A cewar Hukumar, matsalar na kuma lalata kasar noma da lalata hanyoyin ruwa, tare da kuma tilasta alumma, tashi daga matsugunan su, zuwa wasu gurare, domin su ci gaba da gudanar da rayuwarsu.

Hakazalika,  a cikin wasu rahotanni da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar, sun bayyana cewa, a fadin duniya, ana yin amfani da Lidojin da suka kai, yawan miliyan 500 a duk shekara, wanda kusan tan miliyan 13, suke kwarara zuwa cikin Tekuna, a duk shekara.

Ana kuma yin amfani da Gangunan Mai miliyan 17, da aka sarrafa, aka kuma zuba a cikin Gangunan, inda kuma a fadin duniya, mutane ke sayen Kwalaben Man da suka kai miliyan daya.

An kiyasata cewa, a duk shekara, daobboin da ke rayuwa a cikin Tekuna  guda 100,000 ne, irin wadannan Robobin da aka zuba a cikin Tekunan, suke hallaka su.

Bugu da kari, wasu bincike da aka gudanar, sun nuna cewa, Ruwan sha da ake sarrafawa a sanya a cikin Robobin Shan Ruwa, sun kai kaso 90 a cikin dari, inda kuma Ruwan da ake samu daga Fanfuna, suka ke da kaso  83 a ckin dari, wadanda kuma suke dauke da sanadaran microplastic, da ke makalewa, a cikin Robobin, inda wannan sanadarin, ke shafar kiwon lafiyar bil Adama.

A Nijeriya za a iya cewa, kalubalen na muhalli sun kasance iri-iri, musamman duba da annobar ambaliyar ruwan sama da kasar ke fuskanta a duk lokacin damina da Fari da gurrbatar muhalli da kuma rashin samar da kyakyawan tsarin zubar da shara, musamman na bolar Robobin da aka gama amfani da su.

Misali, a ranar 28 na watan Mayun 2025, garin Mokwa, da ke a jihar Neja, an fuskanci, mummunar ambaliyar ruwan sama, inda jami’ai suka sanar da cewa, sama da mutane 200 da iftila’in ya aukwa, suka rasu tare da kuma bacewar mutane da yawansu ya kai sama da 1,000, wasu 121 suka samu raunuka, gidaje 2,000 suka lalace.

Irin wannan iftila’in na Mokwa, na daya daga cikin rin wadanda suka auku a shekarun baya a wasu sannan kasar.

Ana nan, muma mun goyi bayan furucin da Ministar Kula da Jindadi da Walwalar Mata Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim ta yi, na ciwar kalubalen na gurbatar muhlaii, na janyo tarwatsa alumomin kasar, daga matsugunan su, musamman duba da yadda iftila’in, yafi shafar mata da yara.

Batun da ake yi na samar da wadataccen abincin a kasar, zai kasance ne tamkar wani mafarki, matukar mahukutna kasar, ba su yi gaggawar daukar matakan da suka kamata, kan batun na gurbatar muhalli, a kasar ba.

Domin samar da tsarin rage zubar da bola, musamman ta Robobi a kasar Gwamnatin Tarayya ta gabatar da wani tsari na  NPPWM.

Sai dai, wannan tsarin ya hadu da cikas, musamman duba da cewa, wanzar da tsarin daga bangaren Gwamnatin, ba ta mayar da hankali akansa ba, inda sai dai kawai, daidaikun ‘yan kasar ne a kashin kansu suke ci gaba da tsaftace guraren da ake jibge bola, musamman a birane da wasu guraren.

Shugabar Babban Majalisi a Majalisar Dinkin Duniya Maria Fernanda Espinosa Garcés, ta bayar da shawarar cewa, batun na gurbar muhalli, abu ne, da ya wajaba a sake tunani akai.

A daukacin jihohi 36 na kasar, Legas da Ekiti ne kawai, suka dauki matakan da suka kamata, kan kare gurbatar muhalli, a jihohinsu.

Kazalika, a matakin Majalisa, Shugaban Kwamiti kan Yada Labarai da Kula da Hudda da Jama’a Hon. Akin Rotimi ya shelanta cewa, daga cikin kudurori 899 da Majalisar ta gabatar a cikin shekaru biyu, guda 27 ne kacal, Majalisar ta mayar da hankali kan na kula da muhalli.

Sai dai, an ruwaito cewa, wani Majalisar na kan kokrin samar da wasu tsare-tsare na yakar yawan amfani da Robobin barkatai a kasar, musamman a biranen kasar.

A ra’ayin wannan Jaridar, muna goyon bayan cewa, ba zai yuwa a bar Nijeriya a baya, wajen shiga cikin kokarin da ake yi, a fadin duniya, na yakar gurbata muhalli ba.

Ya zama wajbi, bikin na wannan shekarar, ya kasance mataki na farko, na yakar gurbata muhalli, ba wai kawai tatsuniya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

August 29, 2025
Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Next Post
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta'adda, Sun Kashe 8 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version