Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Boko Haram: Buni Ya Umarci SEMA Ta Kai Agajin Gaggawa A Geidam

by Muhammad
January 9, 2021
in RAHOTANNI
2 min read
SEMA
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela,

Biyo bayan farmakin da mayakan Boko Haram suka kai a garin Gaidam ranar Laraba, Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya umurci hukumar SEMA ta kai wa jama’ar da farmakin ya shafa tare da kokarin gano kimar asarar da harin ya haifar.

samndaads

Ranar Laraba mayakan sun farmaki garin Gaidam ranar dauke da makamai masu sarrafa kansu, wanda ya jawo asarar dimbin dukiyar jama’a.

Gwamna Buni ya sanar da hakan ta hanyar ofishin Daraktansa na yada labarai, Mamman Mohammed, Buni ya fara da bayyana alhininsa ga jama’ar Gaidam dangane da harin wanda ya bayyana a matsayin wanda ya mayar da hannun agogo baya a ci gaban da ake samu na maysalar tsaro da kokarin jihar wajen sake farfado da yankunan da abin ya shafa a baya.

Bugu da kari, ya umurci jami’an SEMA su garzaya zuwa garin domin bayar bai wa jama’ar Gaidam agajin gaggawa tare da kiyasta asarar da farmakin ya jawo.

A nashi bangaren, shugaban SEMA, Dr Mohammed Goje, ya shaidar da cewa tuni sun fara aiwatar da umurnin Gwamnan tare da bayar da tabbacin fara aikin tattara bayanai dangane da farmakin da ayyukan jinkan jama’a.

A nashi bangaren kuma, jami’in hulda da jama’a na rundunar yan-sandan jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim, ya shaida wa manema labarai a jihar tabbacin kai harin tare da dawo da doka da oda a garin.

Ya ce an kona motoci guda biyu wadanda suke kyautata zaton na mayakan Boko Haram ne a lokacin artabun.

“Haka kuma, yan ta’addan sun kona gida tare da shaguna guda uku, tare da sace magunguna daga babbar asibitin garin da mota kirar Hilux daya mallakar jami’an tsaron jar-kwala.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Daukar Ma’aikata: NDLEA Ta Fitar Da Jerin Sunayen Wadanda Suka Yi Nasara

Next Post

Gwamnan Nasarawa Ya Kafa Kwamitin Jarabawar Zama Sakatare

RelatedPosts

Alaba

‘Yan Kasuwan Arewa A Legas Mu Hada Kai Don Cigaba – Muhammadu Alaba

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Hadin kai shi wani babban al’amari...

Jama'a

Taimaka Wa Jama’a Shi Ne Shugabanci Nagari -Matawalle Alagwadun Legas  

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai,   Matawallen Alagbado, Alhaji Muhammadu ya...

Samarun

Yadda Rasuwar Matashi Ta Jefa Mutane Cikin Alhini A Samarun Zariya

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Idris Umar, A ranar laraba ta wannan makon da...

Next Post
Sakatare

Gwamnan Nasarawa Ya Kafa Kwamitin Jarabawar Zama Sakatare

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version