Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Boko Haram: Gwamna Zulum Ya Nuna Damuwarsa A Kan Sabbin Hare-Hare A Borno

by
2 years ago
in LABARAI
2 min read
Liverpool Ta Lallasa Ta Lallasa Machester City
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

A ci gaba da samun kai sabbin hare-haren mayakan Boko Haram a jihar Borno, Gwamnan jihar, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya umurci shugabanin kananan hukumomin jihar da cewa su hada hannu wuri guda tare da jami’an tsaro wajen aikin tunkarar kalubalen sabbin hare-haren da mayakan Boko Haram ke yi a yan kwanakin nan.

Bugu da kari kuma, Gwamnan ya bayyana matukar damuwar sa dangane da koma bayan lamarin tsaro da ake samu a jihar a yan kwanakin nan, musamman a wasu garuruwa da kauyukan karamar hukumar Askira-Uba a jihar.

A cikin makon nan ne dai mayakan na Boko Haram suka kai sabon farmaki a garin Chul, da mabambantan hare-hare a wasu garuruwa irin su Rumirgo, Lassa, Mussa, Kufa tare da Gwandam, duk a cikin karamar hukumar Askira-Uba.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Gwamnan ya bayyana hakan a cikin wata sanarwar bayanin manema labarai, mai dauke da sa hannun mai taimaka masa ta sha’anin sadarwa da yada labarai-Malam Isa Gusau, inda ya ce, Gwamna Zulum ya bayyana hakan dangane da yanda maharan ke takure a yankin arewacin jihar Borno, amma kuma za su iya ratsa kowane bangaren jihar.

Mista Gusau ya ce, “Gwamna Zulum ya damu matuka dangane da ci gaba da kai hare-haren Boko Haram suka aiwatar a garuruwan Chul, Rumirgo, Lassa, Mussa, Kufa da Gwandam, duka a cikin karamar hukumar Askira-Uba da ke jihar Borno”.

“Kuma gwamnan ya bayyana tabbacin goyon bayan gwamnatinsa ga jama’ar da wannan lamarin ya shafa, musamman ta fuskar baiwa sojoji kwarin gwiwa hadi da sauran jami’an tsaro, don ci gaba da kasancewa a yankunan don aikin samar da tsaro tare da samun taimakon yan banga da mafarauta da cibilian JTF a dukan wadannan yankuna”.

“A hannu guda kuma, Gwamna Zulum ya umurci daukwacin shugabanin kananan hukumomin jihar a koda yaushe su ci gaba da aiki kafada da kafada tare da jami’an tsaro a yankin su, domin samun nasarar dakile kalubalen tsaron da ya ki ci ya ki cinyewa kana da daukar ingantattun matakan kare rayuwar jama’a da dukiyoyin su, aiki mafi muhimmanci wanda ya rataya a wuya gwamnati”. In ji shi.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Saboda Naki Ba Makwabcin Mu Hadin Kai Ya Lakkada Min Duka Har Na Makance- In Ji Wata Mata

Next Post

Ciyarwa Na Kara Bunkasa Ilimi A Gezawa

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
3 hours ago
0

...

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan  Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

by Sulaiman Idris
4 hours ago
0

...

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Kisa Kan Zargin Batanci Ga Annabi: An Tsare Wadanda Aka Kama A Gidan Gyara Hali

by
5 hours ago
0

...

An Yi Lugudan Wuta Ta Jiragen Yaki Kan Isis An Kashe Kwamandanta Bin-umar A Tabkin Chadi

Dakarun MNJTF Sun Yi Barin Wuta Kan ‘Yan Boko Haram Sun Kashe 300 A Tafkin Chadi

by Leadership Hausa
6 hours ago
0

...

Next Post

Ciyarwa Na Kara Bunkasa Ilimi A Gezawa

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: