Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Boko Haram: Rundunar Soji Ta Kaddamar Da “Operation Tura Ta Kai Bango”

by Muhammad
January 8, 2021
in LABARAI
2 min read
Operation

Daliban sojojin sama na rukunin 4/2019 su na gwada yadda a ke sarrafa babbar bindiga a lokacin bikin yaye su.

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A kokarinta na sake bullo wa lamarin yaki da boko haram ta bayan gida domin samun nasara, Rundunar Sojin Nijeriya ta kaddamar da wata sabuwar dabarar yaki mai suna “Operation TURA TA KAI BANGO”.

Kamar yadda Babban Hafsan Horaswa a rundunar, Manjo Janar NE Angbazo ya bayyana, sabuwar dabarar za ta taimaka wajen kawar da barazanar da sababbin hare-haren boko haram da ISWAP ke yi a yankin arewa maso gabas.

samndaads

Babban Hafsan Horaswar wanda ya wakilici Shugaban Rundunar Sojin, Laftnar Janar Tukur Yusuf Buratai a wajen kaddamar da sabuwar dabarar a shalkwatar birged da ke Buni Gari a Jihar Yobe, ya ce dabarar za ta zama hayaki fid da na kogo ga ‘yan boko haram da takwarorinsu daga mabuyarsu tare da cafke su ko gamawa da su domin ‘yan kasa su samu sukunin kai komo.

“Operation TURA TA KAI BANGO tana da sabon tsaro na tsaro ta yadda za ta kara wa jarumai kaimi a karkashin dabarar yaki ta operation Lafiya Dole domin dakarun sojin Nijeriyar su ji dadin fatattakar sabbin barazanar da boko haram da ISWAP ke yi a yankin arewa maso gabas na kasar nan. A karkashin sabuwar dabarar, za a mayar da hankali ne kacokam a kan mabuyar tsageran… a karshen lokacin da aka diba na amfani da dabarar, ana sa ran ‘yan kasa za su samu walwala ta kai komo tare da gudanar da harkokinsu na yau da kullum kamar noma da kasuwanci cikin kwanciyar hankali,” in ji Manjo Janar Angbazo.

Rundunar dai ta ce tuni aka fara aiki da sabuwar dabarar a ranar 3 ga watan Janairun 2021 kuma har abin ya fara haifar da da mai ido.

SendShareTweetShare
Previous Post

Riga-kafin Korona: Atiku Ya Samu; Talakawa Ko Oho Ko? In Ji ‘Yan Nijeriya

Next Post

Sojojin Sama Na Ci Gaba Da Hana Boko Haram Sakat A Borno

RelatedPosts

Katin Zama Dan Kasa

Nijeriya Ta Wajabta Wa Jami’an Diflomasiyya Mallakar NIN

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

A jiya Lahadi Gwamnatin Tarayya ta shaida cewar, ya zama...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Kanawa Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Game Da Zaben Kananan Hukumomin Kano 

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

A ranar Asabar din da ta gabata, 16 ga Janairu,...

Borno

Borno Ta Ware Miliyan N624 Wajen Bai Wa Dalibai 23,776 Tallafin Karatu

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

A kokarin gwamnatinsa na bunkasa ilimi, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa...

Next Post
Sama

Sojojin Sama Na Ci Gaba Da Hana Boko Haram Sakat A Borno

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version