Muhammad Maitela">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Boko Haram: Sabbin Shugabannin Tsaro Sun Yi Wa Maiduguri Tsinke

by Muhammad Maitela
February 1, 2021
in LABARAI
1 min read
Boko Haram: Sabbin Shugabannin Tsaro Sun Yi Wa Maiduguri Tsinke
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A karon farko bayan da Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya nada sababbin shugabanin rundunonin sojojin Nijeriya, sun kai ziyarar aiki a cibiyar yaki da Boko Haram ta Lafiya Dole (Theatre Command) da ke birnin Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, a ranar Lahadi.

Sabbin manyan hafsoshin sojojin, wadanda su ka kunshi Babban Hafsan Tsaron kasa, Manjo Janar Lucky Iraboh; Babban Hafsan Dakarun kasa, Manjo Janar Ibrahim Attahiru; Babban Hafsan Dakarun Sama, Air bice Marshal Isiaka Amao, hadi da Babban Hafsan Dakarun Ruwa, Rear Admiral Auwal Gambo, tare da sauran manyan kusoshin shalkwatar tsaron kasar.
Bugu da kari, ana sa ran za su gudanar da muhimman tarukan keke-da-keke tare da duk wani mai ruwa da tsaki wajen samun madafa da kara wa juna sani dangane da matakan da suka dace a dauka kan yakin da ake yi da matsalar tsaron.
Har wala yau, wata majiyar tsaro ta bayyana cewa, ana kyautata zaton za su yi amfani da wannan ziyarar ne wajen tattauna kwararan batutuwa tare da fitar da sabbin matakan da za a fuskanci yaki da matsalar tsaron tare da kai wa ga samun cikakken zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas bakidaya.
A hannu guda kuma, bayan kammala kai ziyarorin da sabbin shugabannin sojojin suke gudanarwa, wanda ya hada da sharkwatar bayar da umarni a aikin sojoji tare da sansanin sojoji na din-din-din a barikin Maimalari dake birnin Maiduguri, kana kuma sun ziyarci Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, hadi da fadar Mai Martaba Shehun Borno, Alhaji Abubakar Garbai El-Kanemi, a duka a lokacin ziyarar tasu.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda ’Yan Ta’adda Suka Afka Wa Kauyukan Zuru

Next Post

Yadda Ake Yi Wa Jama’a Alluran Riga Kafin COVID-19 Ya Nuna Aminci Da Nagartar Alluran Kasar Sin

RelatedPosts

Sarkin Musulmi

Fulani Ba ‘Yan Ta’adda Ba Ne –Sarkin Musulmi

by Muhammad Maitela
16 hours ago
0

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya ce...

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

by Muhammad Maitela
21 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gusau A shirin Gwamnatin Jihar Zamfara na...

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

by Muhammad Maitela
21 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Mohammed, Matawallen...

Next Post
Yadda Ake Yi Wa Jama’a Alluran Riga Kafin COVID-19 Ya Nuna Aminci Da Nagartar Alluran Kasar Sin

Yadda Ake Yi Wa Jama’a Alluran Riga Kafin COVID-19 Ya Nuna Aminci Da Nagartar Alluran Kasar Sin

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version