Muhammad Maitela">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Boko Haram Sun Yi Garkuwa Da Matafiya 35 A Kan Hanyar Damaturu-Maiduguri

by Muhammad Maitela
December 20, 2020
in LABARAI
2 min read
Hanyar Damaturu-Maiduguri
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Majiyoyin da wakilinmu ya tattara sun bayyana yadda wasu mayakan da ake kyautata Boko Haram ne sun yi awon gaba da akalla matafiya 35 a kan hanyar Damaturu zuwa Maiduguri.

Bugu da kari, bayanan sun kara da cewa, maharan sun farmaki kwambar motocin matafiyan kusa da Garin- Kuturu wanda yake dab da garin Jakana, a kan hanyar Damaturu zuwa Maiduguri da misalin 5:00 na yammacin ranar Jummu’a.

samndaads

A hannu guda kuma, maharan sun harbe wata mata har lahira; a cikin motar safa-safa ta ‘Borno Edpress’ tare da cinna wa motoci bakwai wuta a lokacin da su ka kai wannan harin.

Ganau a farmakin ya bayyana cewa yan ta’addan sanye da kakin sojoji, sun datse babbar hanyar wadanda suka zo da motoci kirar Hilud biyar, wanda daga nisani su ka yi awon gaba da matafiyan.

“Wanda karasuwar su kusa da inda motar ke da wuya, kan ka ce me sun fada tsakiyar maharan dauke da muggan makamai, sannan kuma da suka ga hakan sun yi kokarin ja-da-baya, amma ina, saboda a daidai wannan lokacin maharan sun riga sun yi musu kofar rago.”

“Sannan a hakan wasu fasinjojin su ka tsallake rijiya da baya; su ka gudu cikin daji, amma sun yi awon gaba da 35, sun kona motocin da ba na haya ba biyu tare da babbar mota daya. Haka kuma an bar motoci tara na mutanen da aka yi garkuwan da su a wajen, kana daga bisani kuma an wawushe kayayyakin su.” In ji majiyar wanda bai yarda a bayyana sunan shi ba.

SendShareTweetShare
Previous Post

Mutum Uku Sun Mutu A Wani Harin Kunar Bakin-Wake A Konduga

Next Post

An Gurfanar Da Makanike A Gaban Kotu Bisa Lafin Satar Wayar Hannu

RelatedPosts

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

by Muhammad Maitela
11 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin da aka diba wa ’yan...

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Muhammad Maitela
11 hours ago
0

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin...

Zakzaky

Matar Sheikh EL-Zakzaky Ta Kamu Da Korona, In Ji Danta

by Muhammad Maitela
16 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Matar Shugaban Kungiyar Musulunci a Nijeriya...

Next Post
Makanike

An Gurfanar Da Makanike A Gaban Kotu Bisa Lafin Satar Wayar Hannu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version