Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Boko Haram Ta Kashe Biyar, Ta Sace Da Dama A Kauyen Borno

by
2 years ago
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

Wasu mahara da a ke kyautata zaton Boko Haram ne sun kashe mutane biyar tare da sace wasu fararen hula masu yawa a lokacin da suka kai farmaki a wani kauyan da ke kusa da garin Chibok, ta karamar hukumar Chibok, a Jihar Borno, a kwana guda da bikin ranar Kirsimati, kamar yanda rahotannin ‘yan banga da mazauna wajen suka nuna.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Talata, a kauyan Korogelem, da ke da nisan kilomita 10 da garin Chibok.
Wasu majiyoyin sun ce ‘yan ta’addan sun sanya wuta a gidajen kauyan a bayan da suka kwashe kayayyaki masu amfani da kuma kayan abinci daga cikin su.
A cewar jami’an ‘yan bangan, ‘yan ta’addan sun ci karfin Sojojin da suke a kauyan ne na tsawon awanni a lokacin da fararen hula suka tsre daga kauyan domin neman tsira da rayukan su.
“Sun zo su da yawa ne, suna ta yin harbi ta ko’ina. Mun yi kokarin fafatawa da su, amma sai suka ci karfin mu saboda yawan su.
“Mun rasa mutane biyar a kauyan mu, kuma sun kwashe wasu ‘yan mata da manyan mata sun tafi da su. mun bincike duk dazukan da ke kusa amma har yanzun ba mu gansu ba. a yanzun haka muna zaman jimami ne sabili ma da ga bikin Kirsimati ya zo,” in ji ‘yan bangar.
Wani mazaunin kauyan mai suna, Musa Bitrus, ya shaida wa wakilinmu cewa, maharan sun kwashe dukkanin abincin da suka tanada domin shagalin Kirsimati sun tafi da shi.
“Mugayen mutane ne, sun sace dukkanin kajin da muka tanada domin bikin Kirsimati. Da yawan mu ma duk har sun yanka kajin na su kafin zuwan na su, amma duk sun kwashe sun gudu da su. ba su bar mana komai da za mu yi bikin Kirsimati da shi ba,” in ji Bitrus.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Jigawa Ta Fara Biyan Sabon Tsarin Albashi

Next Post

Hisbah Ta Haramta Daukar Mace Da Namiji Cikin Adaidaita A Kano

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

by
6 hours ago
0

...

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

by
18 hours ago
0

...

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

by Abdulrazaq Yahuza Jere
1 day ago
0

...

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

by Abubakar Abba
2 days ago
0

...

Next Post
Hisbah Ta Haramta Daukar Mace Da Namiji Cikin Adaidaita A Kano

Hisbah Ta Haramta Daukar Mace Da Namiji Cikin Adaidaita A Kano

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: