Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home Tambarin Dimukradiyya

Boko Haram: Zulum Zai Gina Gidaje 500 A Nguro Da Gyara 1,000 A Bama

by Sulaiman Ibrahim
April 8, 2021
in Tambarin Dimukradiyya
1 min read
Boko Haram: Zulum Zai Gina Gidaje 500 A Nguro Da Gyara 1,000 A Bama
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri

A wata ziyarar aiki da Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya kai a karamar hukumar Bama ranar Talata, domin duba bukatu da yanayin ci gaban jama’ar yankin da matsalar tsaro ta daidaita, ya bayar da umurnin gina gidaje 500 a garin Nguro Soye, da ke Bama.

A hannu guda kuma, Zulum ya bayyana kudurin sake gyara gidajen jama’a sama da 1000 a garin, wadanda mayakan Boko Haram suka kona, domin bayar da damar sake tsugunar da yan gudun hijirar yankin.

A lokacin wannan ziyarar, Zulum ya fara da yada zango a fadar Shehun Bama, Mai-martaba Shehu Umar Ibn Kyari Ibrahim El-kenemi, inda ya bayyana makasudin ziyara a garin, wadda ta kunshi gano halin da makarantu a yankin suke ciki tare da shan alwashin aiki tukuru a matakin bunkasa harkar ilimi a kowane mataki, musamman ga kananan yara a fadin jihar Borno.

Haka zalika, Gwamnan ya bai wa Shehun Bama tabbaci dangane da bukatar da ya mika wa gwamnatin jihar na habaka ayyukan gona ga manoma a wannan damina mai zuwa.

Har wala yau kuma, nan take Zulum ya bayar da umurnin daukar matakan da suka dace a fannin harkokin noma a Bama saboda yadda ake samun karin yan gudun hijirar da suke dawowa gida wanda hakan zai taimaka gaya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Fasahar Sadarwar Zamani Za Ta Bunkasa Sauyin Tattalin Arziki – Shugaba Buhari

Next Post

Kamfanin KEDCO Ya Kaddamar Da Sanya Mita Kyauta Karo Na Biyu A Kebbi

RelatedPosts

Jonathan

…Ta Kaure Tsakanin Goodluck Jonathan Da Babangida Aliyu

by Muhammad
3 days ago
0

Abin Da Ya Sa Gwamnonin PDP Suka Yi Wa Jonathan...

Zaben

Sabon Rikici Ya Tashi A APC Ta Legas Sakamakon Zaben Kananan Hukumomi

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Yusuf Shu’aibu, Sabon rikici ya barke a jam’iyyar APC...

Abaribe

Sanata A Karkashin PDP Ya Bayyana Shakkun Yin Zabe A 2023

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Yusuf Shu’aibu, Wani sanatan a karkashin jam’iyyar PDP Abaribe...

Next Post
Kamfanin KEDCO Ya Kaddamar Da Sanya Mita Kyauta Karo Na Biyu A Kebbi

Kamfanin KEDCO Ya Kaddamar Da Sanya Mita Kyauta Karo Na Biyu A Kebbi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version