Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Borno: PDP Ta Yi Tir Da Tsadar Kayan Masarufi Da Matsalar Tsaro A Karkashin APC

by
10 months ago
in Arewa Maso Gabas
1 min read
Borno PDP
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Khalid Idris Doya,

Jam’iyyar adawa ta PDP a Jihar Borno, ta nuna damuwarta matuka dangane da hauhawar farashin kayan masarufi gami da matsalolin tsaro tare da wasu ‘yan batutuwa da suke jibge a karkashin jam’iyyar APC.

PDP tana mai cewa tabbas jama’a suna fama da kuncin neman abun da za su kai bakin salati da kuma kalubalen tsaro da ya jima yana addabarsu wanda an gagara shawo kan su ne a sakamakon gazawar gwamnatin APC.

Labarai Masu Nasaba

Eid-el-kabir: Buni Ya Bunkaci ‘Yan Nijeriya Su Nuna Sadaukarwa Da Hadin Kan Kasa

Babbar Sallah: ‘Yan Sanda Sun Bayar Da Tabbacin Samar Da Tsaro A Yobe 

Shugaban jam’iyyar PDP a Borno, Usman Mahdi Badairi, shi ne ya shaida a jiya lokacin da suke ganawa da shugabannin jam’iyyar na kananan hukumomi tare da mambobi da magoya bayanta a Maiduguri.

Badairi ya jinjina wa mambobin jam’iyyar PDP a bisa aikin hadaka da suke yi wajen kawo cigaban jam’iyyar a matakin jihar, sai ya horesu da su cigaba da hakan domin nasarar jam’iyyar a nan gaba.

Shugaban yana mai bada tabbacin cewa mambobin PDP ba za su yi zabin tumun dare na wadanda suke jagorantarsu a jam’iyyar ba.

Ya kuma nemi mambobin jam’iyyar da su kara hada kansu su ci gaba da zama ‘ya’yan tafiya daya domin kara samar wa jam’iyyar dumbin nasarorin da suka dace.

Daga bisani ya umarci shugabanin jam’iyyar na kananan hukumomi da mambobinsu da su koma kananan hukumominsu domin shirye-shiryen babban taron zaben jam’iyyar da ke tahowa.

“Mun damuwa matuka gaya bisa gazawar gwamnatin APC, ta fuskacin hauhawar farashin kayan abinci, hauhawar matsalar tsaro, rikicin tsarin jama’a, da kuma yawan ciwo bashin da gwamnati ke yi. Wadannan ababen matsaloli ne manya-manya.”

Shugaban ya bada tabbacin cewa dukkanin mambobin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki na PDP sun shaidi yadda daruruwan mambobin APC ke ficewa daga jam’iyyar zuwa PDP, don haka ne ya nemi su kara rungumar jam’iyyar dari bisa dari.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Ambaliya: Gwamnatin Taraba Za Ta Fara Sauya Wa Gidajen Da Ke Bakin Ruwa Matsuguni

Next Post

2023: Tsohon Dan Majalisa Ya Nemi Gwamna Bala Ya Amince Da Takarar Shugaban Kasa

Labarai Masu Nasaba

Eid-el-kabir

Eid-el-kabir: Buni Ya Bunkaci ‘Yan Nijeriya Su Nuna Sadaukarwa Da Hadin Kan Kasa

by
10 months ago
0

...

Kayayyakin Da Aka Wawure

Babbar Sallah: ‘Yan Sanda Sun Bayar Da Tabbacin Samar Da Tsaro A Yobe 

by
10 months ago
0

...

Takarar

2023: Tsohon Dan Majalisa Ya Nemi Gwamna Bala Ya Amince Da Takarar Shugaban Kasa

by
10 months ago
0

...

Taraba

Ambaliya: Gwamnatin Taraba Za Ta Fara Sauya Wa Gidajen Da Ke Bakin Ruwa Matsuguni

by
10 months ago
0

...

Next Post
Takarar

2023: Tsohon Dan Majalisa Ya Nemi Gwamna Bala Ya Amince Da Takarar Shugaban Kasa

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: