CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Brazil Ta Gama Gwajin Allurar Rigakafi Kan Mutane A Mataki Na Uku

by CRI Hausa
December 27, 2020
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Brazil Ta Gama Gwajin Allurar Rigakafi Kan Mutane A Mataki Na Uku
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A kwanakin baya ne, gwamnatin jihar Sao Paulo ta kasar Brazil da cibiyar nazarin harkokin likitanci ta Butantan suka shirya taron manema labarai cikin hadin gwiwa, inda suka sanar da kammala gwajin allurar rigakafin cutar COVID-19 ta CoronaVac da kamfanin fasahar halittu na Sinovac na kasar Sin ya gudanar kan mutane a mataki na uku.

Sakamakon ya nuna cewa, wannan allurar rigakafin cutar COVID-19 ta yi kyakkyawan tasiri kan wadanda aka yi yiwa, ba ta da wata illa.
Shugaban cibiyar Butantan Dimas Covas ya ce, gaba daya, an yi wa masu aikin sa kai allurar rigakafin sama da dubu 20, kuma, sakamakon ya nuna cewa, allurar rigakafin cutar COVID-19 ta CoronaVac ta kasance allura mafi tsaro a fadin duniya, ta kuma dace da bukatun hukumar kiwon lafiyar duniya ta WHO, a don haka cibiyarsa za ta gabatar da rokon yin rajista kan wannan allurar rigakafin cutar COVID-19 ta CoronaVac ga hukumar sa ido kan harkokin kiwon lafiyar kasar Brazil.
Jiya da safe, an kai allurar rigakafin cutar COVID-19 ta CoronaVac miliyan 5.5 daga kasar Sin zuwa jihar Sao Paulo. A mako mai zuwa kuma, za a kai Karin allurar miliyan 2 zuwa wannan jiha.
Shugaban ofishin kiwon lafiyar jihar Sao Paulo Jean Gorinchteyn ya ce, bisa shirin da aka tsara, za a fara yi wa al’ummomin jihar allurar rigakafin cutar COVID-19 daga ranar 25 ga watan Janairun shekarar 2021. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Matakin Mallake Allurar Rigakafin COVID-19 Da Kasashen Yamma Ke Dauka Na Lahanta Hadin Kan Kasa Da Kasa Na Yakar Cutar

Next Post

Kafar Yada Labarai Ta Singapore: UAE Ta Amince Da Allurar Rigakafin COVID-19 Da Sin Ta Gabatar

RelatedPosts

Dabarun Gwamnatin Sin Ya Baiwa Duniya Kwarin Gwiwar Tinkarar Kalubaloli

Dabarun Gwamnatin Sin Ya Baiwa Duniya Kwarin Gwiwar Tinkarar Kalubaloli

by CRI Hausa
9 hours ago
0

“Abin da babba ya hanyo yaro ko ya hau kololuwar...

Shugaban Kasar Sin Ya Yiwa Taron Davos Jawabi Ta Kafar Bidiyo

Shugaban Kasar Sin Ya Yiwa Taron Davos Jawabi Ta Kafar Bidiyo

by CRI Hausa
9 hours ago
0

A yau ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya halarci...

Ko Akwai Yiyuwar Kyautata Hulda Tsakanin Amurka Da Turai Bayan Sabon Shugaban Kasar Ya Fara Aiki?

Ko Akwai Yiyuwar Kyautata Hulda Tsakanin Amurka Da Turai Bayan Sabon Shugaban Kasar Ya Fara Aiki?

by CRI Hausa
9 hours ago
0

Wasu kafofin watsa labarai na kasashen Turai sun taba yin...

Next Post
Kafar Yada Labarai Ta Singapore: UAE Ta Amince Da Allurar Rigakafin COVID-19 Da Sin Ta Gabatar

Kafar Yada Labarai Ta Singapore: UAE Ta Amince Da Allurar Rigakafin COVID-19 Da Sin Ta Gabatar

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version