BRICS Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Nahiyar Afirka
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

BRICS Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Nahiyar Afirka

byCMG Hausa
2 years ago
brics

Ga duk mai bibiyar yanayin ci gaban da ake samu karkashin hadakar kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen BRICS, zai tabbatar da cewa kungiyar ta haifar da kyakkyawan fatan cimma moriyar juna, matakin da ke kara kyautata moriyar kasashen Afirka, da sauran kasashe masu tasowa. 

Kungiyar BRICS mai kunshe da kasashen Brazil, da Rasha, da Indiya, da Sin da Afirka ta kudu, wadda a yanzu ke shirin karkare taron shugabanninta karo na 15 a Afirka ta kudu, ta tabbatar da matsayinta na adawa da ra’ayin cacar baka, da danniya, ta kuma mai da hankali ga yayata akidun gudanar da cudanya tsakanin dukkanin sassa, da martaba juna, da hadin gwiwa, da rike gaskiya da adalci, ta hanyar samar da wani ginshiki na daban, wanda duniyar yau za ta iya dogaro da shi.

  • Me Ya Sa Nijeriya Ke Neman Shiga Tsarin BRICS?

Ya zuwa yanzu, kasashe mambobin kungiyar BRICS ne ke da sama da kaso 40 bisa dari na jimillar adadin al’ummar duniya, da kaso 20 bisa dari na darajar cinikayyar duniya, yayin da kasashe mambobin take janyo kaso 25 bisa dari na daukacin jarin waje da ake zubawa a duniya.

La’akari da alakar kut da kut ta cinikayya, da musaya tsakanin dukkanin wadannan kasashe mambobin BRICS da kasashen nahiyar Afirka, da kuma tasirin alkaluman tattalin arzikinsu ga bunkasar tattalin arzikin duniya baki daya, za mu iya gane dalilan da suka sanya ci gaban BRICS ke taka rawar gani ga ci gaban Afirka, ta hanyoyi masu yawa.

BRICS ta riga ta gabatarwa duniya wata dama ta cimma alherai, musamman ga kasashen da tattalin arzikinsu ke saurin bunkasa, da kasashe masu tasowa, ta kuma ingiza hadin gwiwarsu, tare da zama wani muhimmin dandali na kyautata ci gaban kasashe masu tasowa ta fuskar dinke dukkanin sassa, yayin tafiya kan tafarkin bunkasuwa tare.

Wadannan dalilai ne suka sanya a halin yanzu, karin kasashen Afirka da suka hada da Najeriya, da Aljeriya da Masar, suka shiga cikin jimillar kasashe 23 dake fatan zama sabbin mambobin wannan kungiya mai daraja.

Yayin da wasu kasashen duniya ke aiwatar da matakan haifar da baraka ga duniya, da kafa tsarin rarrabuwar kawuna, da fadada jibge sojoji, da kafa kawance a fannin, da nufin tabbatar da ikon kashin kai, a hannu guda kungiyar BRICS, na kara mayar da hankali ga bunkasa zaman lafiyar duniya, da yayata manufofin ci gaban bai daya na kasashen duniya, ciki har da kasashen Afirka.

Don haka dai muna iya cewa, yayin da kasashen Afirka ke fafutukar raya kansu, da kaucewa duk wani yanayi na koma baya, kungiyar BRICS ta zama wata hanya mai inganci da kasashe na Afirka za su ci gaba da bi, domin kaiwa ga tudun mun tsira. (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
‘Yan Boko Haram Sun Saki Mata 48 Da Suka Yi Garkuwa Da Su A Borno

'Yan Boko Haram Sun Saki Mata 48 Da Suka Yi Garkuwa Da Su A Borno

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version