Buga Kudi: EFCC Za Ta Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu A Ranar Laraba
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buga Kudi: EFCC Za Ta Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu A Ranar Laraba

bySadiq
1 year ago
EFCC

Hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), za ta gurfanar da tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele a gaban kuliya bisa kashe Naira biliyan 18.96 wajen buga takardun kudi miliyan 684.5.

Tun da farko dai an shirya gurfanar da shi a ranar 30 ga watan Afrilu, 2024, amma aka dage zaman bayan yarjejeniyar da kotu ta yi da bangarorin EFCC da na Emefiele.

  • Gwamnatin Nijeriya Ta Kafa Makarantar Bayar Da Horo Kan Al’adun Ƙasa – NICO
  • Sojar Ukraine Ta Zama Bazawara Kwana Biyu Da Aurenta

A tuhume-tuhume hudu da EFCC ta shigar gaban kotun, ta yi zargin cewa Emefiele ya bijire wa umarnin doka lokacin sauya takardun Naira a lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

EFCC ta kuma zargi Emefiele da cire Naira biliyan 124.8 daga asusun tara kudaden shiga na tarayya ba bisa ka’ida ba.

LEADERSHIP ta tattaro cewa tsohon gwamnan na CBN zai gurfana a gaban mai shari’a Maryann Anenih ta babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Wannan shari’ar za ta kawo adadin tuhume-tuhumen da ake yi wa tsohon gwamnan na CBN zuwa uku.

A ranar 17 ga watan Nuwamba, 2023, Emefiele ya gurfana a gaban mai shari’a Hamza Muazu a kan tuhume-tuhume shida da suka hada da damfara, almundahana, wanda ya ki amsa laifinsa.

An kuma zarge shi da cin zarafin ofishinsa ta hanyar kwangilar sayen motoci 43 da suka kai Naira biliyan 1.2 daga 2018 zuwa 2020.

A ranar 8 ga watan Afrilu, 2024, EFCC ta kuma sake gurfanar da Emefiele tare da wani Henry Omoile a gaban mai shari’a Rahman Oshodi na kotun laifuffuka da ke Ikeja a Jihar Legas, kan zargin almundahanar dala biliyan 4.5 da Naira biliyan 2.8.

Sai dai Emefiele ya musanta wadannan tuhume-tuhume.

Rotimi Oyedepo (SAN) ne, ya sake shigar da sabuwar tuhuma a ranar 2 ga watan Afrilu, 2024 a madadin EFCC tare da wasu lauyoyi takwas da ke aiki da babban lauyan tarayya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Next Post
Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima’i A Benuwe

Matar Aure Ta Kashe Mijinta Saboda Yawan Jima'i A Benuwe

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version