Buhari Ya Umarci Shugabannin Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas Da Su Kama Aiki 
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Umarci Shugabannin Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas Da Su Kama Aiki 

bySulaiman
2 years ago
Buhari

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci membobin sabuwar hukumar gudanarwa ta Hukumar Haɓaka Arewa-maso-gabas (NEDC) da su kama aikin riƙon ƙwarya ba tare da ɓata lokaci ba don kada a bar wajen babu shugabanni.

 

Shugabannin za su yi aiki ne kafin su samu tabbacin naɗin su daga Majalisar Dattawa kamar yadda doka ta tanada.

  • NSCDC Ta Cafke Mutum 9 Kan Zargin Satar Sinadarin Ruwa A Zamfara

Wata sanarwa ga manema labarai da Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Dakta Nasir Sani-Gwarzo, ya rattaba wa hannu ta ce an yanke wannan shawarar ne don kada a bar wajen babu shugabanni.

 

Haka kuma shugaban ƙasa ya amince da cewa sabon Manajan Darakta kuma Shugaban hukumar, Alhaji Umar Abubakar Hashidu, shi ma ya kama aiki a matsayin riƙo kafin ya samu amincewar Majalisar Dattawa.

 

Dakta Gwarzo ya ce hakan ta faru ne bayan ƙarewar wa’adin tsohon shugaban hukumar da sauran membobin a ranar 7 ga Mayu, 2023.

 

A cewar sa, Buhari ya kuma amince wa Lauya Bukar Baale da ya kama aiki a matsayin ciyaman mai riƙon ƙwarya na hukumar tare da membobi 10 na hukumar gudanarwar.

 

Bugu da ƙari, shugaban ya ba da umarni ga jami’in da ke riƙe da ofishin manajan daraktan hukumar a yanzu da miƙa ragamar ga sabon da aka naɗa ba tare da ɓata lokaci ba.

 

Gwarzo ya ce an ba da wannan umarnin ne domin “a kauce wa samun giɓi a wajen gudanar da ayyukan yau da kullum a wannan hukumar mai matuƙar muhimmanci da tasiri kafin lokacin da Majalisar Dattawa za ta ba su tabbacin naɗin su.”

 

Ita dai Hukumar Gudanarwar ta NEDC ta ƙunshi membobi kamar haka: Suwaiba Idris Baba, Babbar Daraktar Harkokin Agaji (daga Taraba, Arewa-maso-gabas); Musa Umar Yashi, Babban Daraktan Gudanarwa da Harkar Kuɗi (daga Bauchi, Arewa-maso-gabas); Dakta Isma’ila Nuhu Maksha, Babban Daraktan Gudanarwa (daga Adamawa, Arewa-maso-gabas), da Umar Abubakar Hashidu, Manajan Darakta/Shugaba (daga Gombe, Arewa-maso-gabas).

 

Sauran su ne Onyeka Gospel-Tony, Memba, (daga Kudu-maso-gabas); Hon. Madam Hailmary Ogolo Aipoh, Memba (daga Kudu-maso-kudu); Eya Kwamanda Babatunde Akanbi (ritaya), Memba (daga Kudu-maso-yamma); Mustapha Ahmed Ibrahim, Memba (daga Arewa-maso-yamma); Hadiza Maina, Memba (daga Arewa-ta-tsakiya), Alhaji Grema Ali, Memba (daga Arewa-maso-gabas), da kuma wakili daga Ma’aikatar Kuɗi, Kasafi da Tsare-tsaren Ƙasa ta Tarayya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Xi Ya Amsa Wasikar Tsoffin Masanan Dakin Adana Kayayyakin Fasaha Na Sin

Xi Ya Amsa Wasikar Tsoffin Masanan Dakin Adana Kayayyakin Fasaha Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version