Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Faruk, Gwamnan Soja Na Farko A Arewaci Maso Yamma

by Khalid Idris Doya
December 20, 2020
in LABARAI
1 min read
Ta’aziyyar Rasuwar Faruk
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Nijeriya, Alhaji Muhammadu Buhari, ya yi ta’aziyyar rasuwar gwamna na farko a zamanin mulkin soji daga shiyyar Arewa Maso Yamma, Alhaji Usman Faruk.

Wakilinmu ya nakalto cewa, marigayi Usman Faruk dai tsohon kwamishinan ‘yan sanda ne, ya rasu ne a shekaran jiya 18 ga watan Disamba. An haifesa ne a shekarar 1935 a garin Gombe, ya zama gwamnan mulkin soja ne a yayin mulkin shugaban kasa a zamanin soja Yakubu Gowon.

samndaads

A sanarwar da shugaban ya fitar ta hannun hadiminsa, Mallam Garba Shehu, Buhari ya shaida cewar tsohon kwamishinan ‘yan sandan ya himmatu wajen hada kan kasa da ‘yan kasa a lokacin da yake raye.

“Shugaba Muhammadu Buhari ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai, ‘yan uwa da abokan marigayi gwamnan farko a zamanin mulkin soji na shiyyar arewa maso yamma, Alhaji Usman Faruk, bisa rasuwa da Allah ya masa.

“Sannan, Shugaba Buhari ya kuma lura da irin kwazon marigayi Alhaji Usman Faruk ta fuskacin bunkasa al’ummarsa har zuwa bayan lokacin da ya yi ritaya, ya nanata cewa marigayin ya kasance mai kwatanci da kyawawan ayyuka gami da hidintuwa wa al’umma.

“Buhari yana masa addu’ar Allah ya jikansa ya sanya aljannace makomarsa, sannan yana addu’ar Allah albarci iyalan da ya bari,” inji sanarwar.

Tun bayan rasuwarsa ne dai wakilinmu ya shaida mana cewar al’umma ke ta cinciridun mika ta’ziyyar rashinsa a jihar gwamna, inda fitattun mutane da dama suka yi ta nuna alheninsu da wannan babban rashin.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Zamu Nemi Karin Mazabun Karamar Hukumar Dala, Inji Babangida Yakudima

Next Post

Shugaban Majalisar Dattijai Ya Taya Shugaba Buhari Murnar Cika Shekara 78 A Duniya

RelatedPosts

Hutun Kirsimeti

Gobarar Sakkwato: Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Tambuwal

by Khalid Idris Doya
7 hours ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Kakkarfar tawagar Gwamnatin Tarayya ta jajantawa...

An Sace Jami’ar Yaɗa Labarun NIS Reshen Jihar Edo

An Sace Jami’ar Yaɗa Labarun NIS Reshen Jihar Edo

by Khalid Idris Doya
10 hours ago
0

Masu garkuwa sun yi awon gaba da jami'a mai magana...

Tsaro: Wasu Gwamnonin Nijeriya Na Ganawa Da Shugabannin Fulani Makiyaya

Tsaro: Wasu Gwamnonin Nijeriya Na Ganawa Da Shugabannin Fulani Makiyaya

by Khalid Idris Doya
11 hours ago
0

Yau gwamnonin yammacin Nijeriya ke gudanar da wani taro da...

Next Post
Shugaban Majalisar Dattijai

Shugaban Majalisar Dattijai Ya Taya Shugaba Buhari Murnar Cika Shekara 78 A Duniya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version