Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

An Bukaci Gwamna Lalong Da Ya Yi Garambawul A Shugabancin Jam’iyyar APC

by Tayo Adelaja
September 12, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga  Lawal Umar Tilde, Jos

Kasa da ‘yan makonni kali’lan a gudanar da zaben kana’nan hukumomi a jihar Filato, an bukaci gwamnan jihar Barista Simon Bako Lalong, da ya yi sauye-sauyen mukamai a gwamnatinsa.

Wani jigo a siyasar jihar mai suna Alhaji Danlami Abubakar ne ya nuna bukatar haka yayin wata ganawa da LEADERSHIP A YAU ta yi da shi kwanan nan a Jos babban birnin jihar.

A cewar Abubakar, ya zama wajibi ga gwamnan da ya yi sauye-sauye a jam’iyyar don ta sami zarafin taka kyakkyawar rawa a zaben kananan hukumomi da ke tafe da ma zabubbukan 2019.

Dagan an, sai ya yaba da dimbin nasarorin da gwamnan ya samu a tsakanin shekaru biyun din da ya yi da kama ragamar mulkin jihar. Sannan ya nuna takaicinsa dangane da yadda da yawa daga cikin wadannan shugabannin saboda son-kai da rashin kishi ya sa sun kasa gudanar da harkokin jam’iyyarsu ta APC a yankunansu, tare da bada misali da karamar hukumar Jos ta Arewa da take cibiyar gwamnatin jihar, inda ya ce mutum zai iya zaga dukkan unguwannin ba zai ga Tutar Jam’iyyar APC mai nuna ofishin jam’iyyar ba balle jama’a su samu wajen kai koke ko shawara.

Ya ce gwamna ya sami nasarori masu dimbin yawa tun hawansa karagar mulkin jihar a 2015 da suka hada da maido da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’ummar jihar, biyan basussukan albashin ma’aikata da fansho wanda ya gada daga tsohuwar gwamnatin da ta gabata ta PDP, da kuma karasa gyra hanyoyi da biyan ‘yan kwangila basussukan da suke bin gwamnati.

Alhaji Abubakar ya yi amfani da wannan dama wajen mika rokonsa ga al’ummar jihar da su kara bai wa gwamnan goyon baya da hadin kai don ya sami sukunin gudanar da dimbin ayyukan inganta rayuwar al’umma da yake kokarin aiwatarwa wadanda suka hada da gyran hanyoyin cikin garin Jos da na karkara da za su hade hedkwatocin kananan hukumomi 17 da Jos babban birnin jihar da gina babbar kasuwar Jos kamar yadda ya sanar wa al’ummar jihar a jawabinsa na farkon kama aiki.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

WALKIYA: Dogaro Da Kai: Kalubale Ga Arewacin Nijeriya

Next Post

Zan Samo Wa Nijeriya Cibiyoyin Koyon Sana’a Daga Jamus —Ambasada Tugga

RelatedPosts

Lantarki

Gwamantin Tarayya Ta Yi Bayani Game Matsalar Karancin Wutar Lantarki A Kasar

by Muhammad
10 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Ministan Wutar lantarki, Injiniya Sale Mamman,...

Direbobi

Satar Mutane A Manyan Hanyoyi: Direbobi A Zamfara Sun Tsunduma Yajin Aiki

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Direbobin abeben hawa na haya masu...

Gwamnonin

Gwamnonin Nijeriya Sun Koka Kan Tabarbarewar Tsaro

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Kungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) ta nuna...

Next Post

Zan Samo Wa Nijeriya Cibiyoyin Koyon Sana’a Daga Jamus —Ambasada Tugga

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version