Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Bukaci Gwamna Lalong Da Ya Yi Garambawul A Shugabancin Jam’iyyar APC

by Tayo Adelaja
September 12, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga  Lawal Umar Tilde, Jos

Kasa da ‘yan makonni kali’lan a gudanar da zaben kana’nan hukumomi a jihar Filato, an bukaci gwamnan jihar Barista Simon Bako Lalong, da ya yi sauye-sauyen mukamai a gwamnatinsa.

samndaads

Wani jigo a siyasar jihar mai suna Alhaji Danlami Abubakar ne ya nuna bukatar haka yayin wata ganawa da LEADERSHIP A YAU ta yi da shi kwanan nan a Jos babban birnin jihar.

A cewar Abubakar, ya zama wajibi ga gwamnan da ya yi sauye-sauye a jam’iyyar don ta sami zarafin taka kyakkyawar rawa a zaben kananan hukumomi da ke tafe da ma zabubbukan 2019.

Ya ce gwamna ya sami nasarori masu dimbin yawa tun hawansa karagar mulkin jihar a 2015 da suka hada da maido da zaman lafiya da hadin kai a tsakanin al’ummar jihar, biyan basussukan albashin ma’aikata da fansho wanda ya gada daga tsohuwar gwamnatin da ta gabata ta PDP, da kuma karasa gyra hanyoyi da biyan ‘yan kwangila basussukan da suke bin gwamnati.

Alhaji Abubakar ya yi amfani da wannan dama wajen mika rokonsa ga al’ummar jihar da su kara bai wa gwamnan goyon baya da hadin kai don ya sami sukunin gudanar da dimbin ayyukan inganta rayuwar al’umma da yake kokarin aiwatarwa wadanda suka hada da gyran hanyoyin cikin garin Jos da na karkara da za su hade hedkwatocin kananan hukumomi 17 da Jos babban birnin jihar da gina babbar kasuwar Jos kamar yadda ya sanar wa al’ummar jihar a jawabinsa na farkon kama aiki.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

WALKIYA: Dogaro Da Kai: Kalubale Ga Arewacin Nijeriya

Next Post

Zan Samo Wa Nijeriya Cibiyoyin Koyon Sana’a Daga Jamus —Ambasada Tugga

RelatedPosts

Hutun Kirsimeti

Gobarar Sakkwato: Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Tambuwal

by Muhammad
10 hours ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Kakkarfar tawagar Gwamnatin Tarayya ta jajantawa...

An Sace Jami’ar Yaɗa Labarun NIS Reshen Jihar Edo

An Sace Jami’ar Yaɗa Labarun NIS Reshen Jihar Edo

by Sulaiman Ibrahim
13 hours ago
0

Masu garkuwa sun yi awon gaba da jami'a mai magana...

Tsaro: Wasu Gwamnonin Nijeriya Na Ganawa Da Shugabannin Fulani Makiyaya

Tsaro: Wasu Gwamnonin Nijeriya Na Ganawa Da Shugabannin Fulani Makiyaya

by Sulaiman Ibrahim
13 hours ago
0

Yau gwamnonin yammacin Nijeriya ke gudanar da wani taro da...

Next Post

Zan Samo Wa Nijeriya Cibiyoyin Koyon Sana’a Daga Jamus —Ambasada Tugga

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version