Bunkasar Cinikin Waje Ta Kasar Sin Ta Wuce Zaton Mutane
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasar Cinikin Waje Ta Kasar Sin Ta Wuce Zaton Mutane

byCMG Hausa
2 years ago
Kasar Sin

Hukumar kwastam ta kasar Sin ta bayyana yau Talata cewa, darajar kayayyakin da kasar ta sayar zuwa ketare a watan Afrilun bana ta kai kudin Sin RMB yuan traliyan 2.02, wadda ta karu da 16.8% bisa na makamancin lokacin bara. Bunkasar darajar kayayyakin da kasar Sin ta sayar zuwa ketare a watan Afrilu ta sake wuce zaton mutane.

Kamfanin dillancin labaru na AP ya ruwaito cewa, ko da yake bukatun da ke akwai a duniya sun yi rauni, amma kasar Sin ta yi fice wajen sayar da kaya zuwa ketare.

  • Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Nadin Sarautar Sarki Charles III

Me ya sa hakan? Saboda gwamnatin kasar Sin ta dade tana kara azama kan manufarta ta bude kofarta ga ketare, da fitar da matakan tabbatar da kwanciyar hankali a cinikin waje.

Tun daga farkon shekarar bana ne hukumomin sassan kasar Sin suka dauki matakan sa kaimi kan bunkasuwar cinikin waje, kana kamfanonin kasar Sin sun je ketare domin neman kwangiloli.

A karshen watan Afrilu kuma, gwamnatin Sin ta fitar da wasu sabbin matakai, ciki had da maido da shirya shagulgula a zahiri a gida, shirya tattaunawa tsakanin kamfanonin kera motoci da kamfanonin jigilar kaya cikin jiragen ruwa, da goyon bayan kamfanonin cinikin waje su yi ciniki ta yanar gizo tsakanin kasa da kasa da kuma habaka hanyoyin sayar da kayayyaki. Dukkan matakan suna da amfani da dacewa, tare da samarwa kamfanonin cinikin waje sabbin damammakin ci gaba.

An yi imanin cewa, sakamakon gudanar da shagulgula da dama a gida, da kara saukaka yin mu’amala a tsakanin mutane, da kuma rika yin kirkire-kirkire a harkokin ciniki, kasar Sin za ta samu karin kuzari kan raya cinikin waje, kuma za ta kara aikewa duniya alamar saurin farfadowar tattalin arzikinta. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2, Sun Kwato Makamai A Anambra

Jami'an Tsaro Sun Kashe Mahara 2, Sun Kwato Makamai A Anambra

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version