Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD

byMuhammad
3 years ago
Burinmu

Cibiyar da ke shirya bita da wayar da kan al’uma kan fasahar sadarwa ta zamani (CITAD) tare da hadin guiwar cibiyar (Hope Action Progress), sun shirya wani taron bita da wayar da kan mata da matasa a Kano kan sha’anin mulki da siyasa da yadda ake gudanar da mulki da hulda da Jama’a.

Cibiyar ta gudanar da taron ranar Litinin a Otel din Tahir da ke Kano, ta kuma bayyana cewa ce a baya ta gudanar da irin wadannan bitoci ga mata da matasa don su fahimci muhimmancin shiga cikin harkokin mulki da sha’anin siyasa a dama da su wurin neman madafun iko.

  • Burinmu Mata Da Matasa Su Fito A Dama Da Su A Harkokin Mulki Da Siyasa — CITAD
  • Ana Rade-Radin APC Ta Tsayar Da Ahmad Lawan A Matsayin Dan Takarar Masalaha

Babbar daraktar shirye-shirye a cibiyar (AAN) kuma guda cikin masu gabatar da kasidu a taron, Suwaiba Muhammad Dankabo, ta bayyana cewa, idan zaka shiga cikin harkokin siyasa kana mai goyan baya ko kuma tsaya wa ka yi a zabe ka, kana da bukatar sanin wasu muhimman al’amura.

Dankabo, ta ce wannan dalilin ne ma yasa suka shirya bita don ilimantar da mata da matasa idan sun samu mulki su san yadda za su tafiyar da shi da yadda za su yi mu’amala da Jama’a.

Da aka tambaye ta shin yanzu kwalliya na biyan kudin sabulu a irin wadannan taruka da suke shirya wa, sai ta kayara da baki ta ce,” Tabbas kwalliya ta fara biyan kudin sabulu don kuwa mun zauna da shugabannin Jam’iyyu a baya kan su ba mata da matasa damar shiga a dama da su a sha’anin mulki da siyasa, suma su tsaya takara a zabe su,”

“Yanzu haka wasu Jam’iyyun sun amsa wannan kiran namu don ko Jam’iyyar PRP a kasa ta ba kaso mai tsoka a matakai daban-daban a takara, haka takwararta Jam’iyyar YPP ta ba mata da matasa akalla 70 tikitin takara, ita ma Jam’iyyar PDP ta ba mata biyu damar tsayawa takara,” in ji Suwaiba.

“Babban Kudurinmu shi ne, a bawa mata da matasa damar su fito su tsaya takara kuma a zabe su a madafun iko daban-daban a Nijeriya ta yadda za su samar da aiyukan yi da tsakulo matsalolin al’uma da magance su, saboda mutumin da yake da damar mulki ya fi kowa kwazon kawo sauyi a cikin al’uma.” A Cewar Dankabo.

A nasa jawabin shugaban Jam’iyyar PRP na Jihar Kano, Abba Sule Namatazu, ya ce Jam’iyyarsu ta PRO tuni ta amsa wannan kiran don kuwa sun ba matasa kaso 75 cikin 100 damar tsayawa takara a kujeru daban-dabn kuma dan takararsu na Kano ma matashi ne mai karancin shekaru, kuma sun ba mata biyu kujerar wakilci a tarayya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman
Kananan Labarai

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

May 23, 2025
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

April 18, 2025
Next Post
Sin Na Shan Yabo Kan Gudunmawarta Ga Kare Muhallin Duniya

Sin Na Shan Yabo Kan Gudunmawarta Ga Kare Muhallin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version