Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home TATTALIN ARZIKI

CBN Ya Gabatar Da Sabbin Cajin Kudi Mai Amfani Da Lambar ‘USSD’

by Sulaiman Ibrahim
March 17, 2021
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Bankuna
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mahdi M. Muhammad, Abuja

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya gabatar da tsarin sabbin caji ga kwastomomi masu amfani da lambar USSD a wayoyinsu wajen aiwatar da hada-hadar kudi na banki.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Talata, kuma dauke da sa hannun mukaddashin daraktan bankin na bangaren sadarwar, Osita Nwanisobi, da daraktan hulda da jama’a na hukumar sadarwa ta Nijeriya, Ikechukwu Adinde.
A cewar sanarwar, kwastomomi za su rinka biyan Naira 6.98 a kan kowace ciniki a duk lokacin da suka yi amfani da lambar USSD.
Sanarwar ta kara da cewa, “Muna farin cikin sanar da cewa bayan cikakken tattaunawa kan muhimman batutuwan, an amince da tsarin kuduri wanda zai yarda da dukkan bangarori.”
“Daga 16 ga Maris, 2021, lambar USSD na hada-hadar kudi da aka gudanar a DMBs (Deposit Money Banks) da dukkan cibiyoyin da ke da lasisi na CBN za a caje su kan kudi N6.98 a kowace ciniki. Wannan ya maye gurbin tsarin biyan kudi na kowane zama na yanzu, yana tabbatar da tsada mai yawa mai sauki ga kwastomomi don bunkasa hada hada-hadar kudi. Wannan tsarin kuma na nuna gaskiya, kuma zai tabbatar da adadin ya zama iri daya, ba tare da la’akari da yawan zaman da aka yi ba,” inji sanarwar.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Don inganta nuna gaskiya a cikin Gwamnatinta, za a tattara sabbin cajin na USSD a madadin MNOs (Masu ba da hanyar sadarwar waya), kai tsaye daga asusun banki na abokan ciniki. Bankuna ba za su sanya karin caji a kan kwastomomi a gare mu na hanyar USSD ba.”
A makon da ya gabata ne Gwamnatin Nijeriya ta bukaci kamfanonin sadarwa da su dakatar da shirinsu na dakatar da ayyukan USSD a kan bashin Naira biliyan 42 da bankuna ke bin su.

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Sanda Sun Ceto ’Yan Mata Masu Ciki Yayin Da Aka Bankado Masana’antar Jarirai

Next Post

Shan Lemon Da Wa’adinsa Ya Kare Ya Yi Ajalin Mutum Uku A Kano, 183 Sun Kwanta Jinya

RelatedPosts

Kudade

Akwai Isassun Kudade Ga Masu Kasuwanci, Cewar CBN

by Muhammad
3 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Babban bankin Nijeriya (CBN) ya kawar...

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad Ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce,...

Hukumar EFCC Ta Gargadi Masu Amfani Da Na’urar ‘POS’ Kan Gurbatacciyar Hada-hada

Hukumar EFCC Ta Gargadi Masu Amfani Da Na’urar ‘POS’ Kan Gurbatacciyar Hada-hada

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad Hukumar nan da ke yaki da...

Next Post
Shan Lemon Da Wa’adinsa Ya Kare Ya Yi Ajalin Mutum Uku A Kano, 183 Sun Kwanta Jinya

Shan Lemon Da Wa’adinsa Ya Kare Ya Yi Ajalin Mutum Uku A Kano, 183 Sun Kwanta Jinya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version