Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

CBN Za Ta Cigaba Da Bai Wa Manoman Shinkafa Bashi – Emefiele

by
2 years ago
in NOMA
1 min read
Kokarin Babban Bankin Nijeriya Na Bunkasa Noman Kwakwar Manja A Kasar Nan
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Za mu cigaba da goyon bayan manoman dake noman shinkafa a kasar ta hanyar ba su bashi a karkaahin shirin aikin noma na Anchor Borrowers.

Furucin ya fito ne daga bakin Gwamnan Babban Banki Nijerya CBN Godwin Emefiele a hirarsa da manema labarai jim kadan bayan kammala taro da masu ruwa da tsaki a fannin noma a babban birinin tarayyar Abuja.

Mista Emefiele ya ce, “Za mu cigaba da goya ba su goyon baya ta hanyar ba su bashi a karkaahin shirin aikin noma na ‘Anchor Borrowers’, domin su ma su na bayar da babbar gudunmawa wajen samar da abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasar nan.”

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar Noman Koko Za Ta Noma Tan 500,000 A Shekarar 2024

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

Gwamnan ya cigaba da cewa, gwamnati za ta goyi bayan masu noman shinkafa don kau da haramtacciyar hanyar shiga da kaya cikin kasar da kuma bunkasa sashin samar da isasshen abinci.

Gwamnan CBN na ya yi kira ga al’umma da su goyi bayan rufe iyakar da gwamnatin ta yi, inda ya ke cewa gwamnatin ta dauki matakin ne don amfanin su Babban Bankin Nijeriya (CBN).

Ya bukaci manoman shinkafa a fadin kasar da kada su kara farashin shinkafa saboda garkame iyakar iyakokin Nijeriya da gwamnati ta sanaya aka yi. Ya bukaci yayan kungiyar manoman shinkafa na kasa RIMAN da sauran masu ruwa da tsaki a sana’ar da kada su boye shinkafa.

Gwamnatin Nijeriya ta rufe iyakar kasar ta a watan Agusta, inda take bayanin cewa a hakan ne za ta binciki shigo da kayayyaki ta haramtacciyar hanya.

Yayin da ya ke bayyana ra’ayinsa kan lamarin, Emefiele yace gwamnatin Tarayya ta dauki matakin ne don bunkata tattalin arziki da kuma tabbatar da cewa kasar ta cimma isasshen abinci musamman a fannin noman shinkafa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Gombe Ba Za Ta Yi Sakaci Wajen Tallafa Wa Manoma Ba

Next Post

ECOWAS Ta Goyi Bayan Tazarcen Adesina A Bankin AfDB

Labarai Masu Nasaba

koko

Kungiyar Noman Koko Za Ta Noma Tan 500,000 A Shekarar 2024

by Abubakar Abba
8 hours ago
0

...

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

Sharhi: Rashin Karfafa Noman Auduga Tamkar Kamun Gafiyar Baidu Ne Ga Nijeriya

by Abubakar Abba
2 weeks ago
0

...

Rogo

Noman Rogo: Yadda Nijeriya Ke Asarar Naira Tiriliyan 27 A Kasuwar Duniya

by Abubakar Abba
3 weeks ago
0

...

Gurjiya

Sirrin Noman Gurjiya Wajen Bunkasa Tattalin Arziki

by Abubakar Abba
4 weeks ago
0

...

Next Post
Rahoton Musamman Kan ‘Yan Nijeriya Da Ke Mulkar Duniya

ECOWAS Ta Goyi Bayan Tazarcen Adesina A Bankin AfDB

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: