CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

bySadiq
3 years ago
CDD

Cibiyar Dimokuradiyya da Ci Gaba ta (CDD), ta yi Allah-wadai da cin tarar Naira miliyan biyar da Hukumar Yada Labarai ta Kasa (NBC) ta yi ga gidan talabijin na Trust TV da wasu kafafen yada labarai uku, saboda watsa shirye-shiryen da suka shafi ‘yan ta’adda.

Trust TV mallakin kamfanin Media Trust Group ne,kamfanin da ke buga jaridun Daily Trust, Aminiya da sauransu.

  • Mu Kula Da Wayoyin Da Ke Hannun Yara
  • Tsadar Man Dizil Na Barazana Ga Masu Kiwon Tarwada A Edo

Haka nan NBC ta ci tarar kamfanin Multichoice Nigeria Limited, mamallakan DSTV, TelCom Satellite Limited (TSTV) da NTA-Startimes Limited, saboda watsa wani shiri da hukumar yada labarai ta BBC ta yi mai taken, ‘Bandits Warlords Of Zamfara’.

CDD, a cikin wata sanarwa a ranar Asabar da Daraktarta, Idayat Hassan ta fitar, ta bayyana sanya tarar a matsayin abin zalunci, inda ta bukaci hukumar ta janye matakinta cikin gaggawa.

A cewar Hassan, tarar wani yunkuri ne na cin mutuncin kafafen yada labarai da kuma tauye hakkin ‘yan kasa na fadin albarkacin bakinsu da yada labarai.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mun yin Allah wadai da kakkausar murya kan tarar da Hukumar Yada Labarai ta Kasa (NBC) ta yi ga gidan talabijin na Trust TV da sauran kafafen yada labarai.

“Mun yi mamakin daukar matakin ba tare da bai wa kafafen yada labaran da abin ya shafa lokaci ba don mayar da martani don kare kansu.

“A matsayinmu na abokan aikin gidan talabijin na Trust TV wajen shirya shirin, ba tare da neman afuwa ba mun jaddada cewa an yi shirin ne kuma an watsa shi ne domin amfanin jama’a. An gina shirin ne bisa tsawon shekaru da aka shafe ana gudanar da bincike a fagen, wanda ke wakiltar dukkanin al’ummomin da abin ya shafa da kuma samar da hanyoyin kawo karshen rikicin.

“Yayin da babban zaben 2023 ke karatowa, muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta guji yin duk wani abu da zai kawo barazana ga harkar yada labarai ko kuma tauye ‘yancin fadin albarkacin baki da ‘yancin ‘yan kasa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
An Nemi Jam’iyyar APC Ta kara kaimi Wajen Biyan Bukatun ‘Yan Nijeriya

An Nemi Jam'iyyar APC Ta kara kaimi Wajen Biyan Bukatun 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version