Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Champions League: A Istanbul Za A Buga Wasan Karshe  Na Shekarar 2022

by
10 months ago
in WASANNI
2 min read
Champions League
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Hukumar kula da gasar cin kwallon kafa ta nahiyar turai ta bayyana filin wasan da zai karbi bakuncin wasan karshe na gasar cin kofin zakarun turai wato Champions League a shekara ta 2023.

Babban kwamitin hukumar kwallon kafar Turai ne ya amince da filin Ataturk Olympic a Instambul ya karbi bakuncin wasan karshe na gasar Zakarun Turai a 2023 bayan nazari a kan filin wasan tun a shekarar data gabata.

Wannan filin da ke Turkiya ne ya kamata ya karbi fafatawar karshe tsakanin kungiyoyin Chelsea da Manchester City, amma aka dage karawar zuwa birnin Porto na kasar Portugal a wasan na karshe 2021.

Labarai Masu Nasaba

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

Hakan ya biyo bayan dokar kasa da kasa domin hana yada cutar korona, kuma Burtaniya ta ayyana Turkiya cikin wadanda annobar ke barazana a lokacin hakan yasa hukumar kwallon kafa ta turai ta canja zuwa filin wasa na Estadio de Dragoa na kungiyar FC Porto.

Haka kuma kwamitin ya tsayar cewar cikin watan Agusta za a yi bikin gudanar da jadawalin Champions League da gasar Europa league da kuma sabuwar gasar Conference League na gasar da za a fara nan gaba.

Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ce ta lashe kofin Champions League na kakar da aka kammala, bayan da ta doke abokiyar hamayyarta daga kasar Ingila, Manchester City a Porto, Portugal.

Sannan kuma an bayyana sauran wuraren da za a yi karawar karshe a Champions League shekaru uku nan gaba bayan da tun farko wasan karshe da ya kamata a yi a Munich a shekarar 2023, yanzu za a yi ne a shekarar 2025.

Har ila yau, filin wasa na Wembley dake London zai gudanar da fafatawar karshe a Champions League a shekarar 2024, kamar yadda aka tsara a baya in ji hukumar ta nahiyar turai.

Daga karshe birnin Dublin ne zai karbi wasan karshe a Europa League a shekarar 2024, shi kuwa Bilbao zai karbi bakuncin gumurzun karshe a karawar mata a shekarar 2024 da na Europa League a shekarar 2025.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Noma A Nijeriya Na Tallafa Wa Tattalin Arzikin Kasar – Hukumar Abinci

Next Post

An Kama Wasu Bisa Zargin Nuna Wa ‘Yan Wasan Ingila Wariyar Launin Fata

Labarai Masu Nasaba

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
0

...

barcelona

Barcelona Ta Sa Hukumar La Liga Asarar Makudan Kudade

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
0

...

Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

by Abba Ibrahim Wada
5 days ago
0

...

Next Post
Wariyar Launin Fata

An Kama Wasu Bisa Zargin Nuna Wa 'Yan Wasan Ingila Wariyar Launin Fata

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: