Cibiyar Noma Za Ta Samar Da Ingantaccen Irin Farin Wake 
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Noma Za Ta Samar Da Ingantaccen Irin Farin Wake 

byAbubakar Abba
1 year ago
Noma

Cibiyar kula da harkokin noma ta kasa da kasa (IITA), ta shirya taron bita na kwana biyu; domin sama wa kanannan manoman kasar nan ingantacen Iri na Farin Wake.

Wani kwararre a fannin samar da Irin noma a cibiyar ta IITA, Farfesa Lucky Omoigui ya bayyana cewa, an shirya taron ne don kokarin hada masu ruwa da tsaki a wannan fanni na samar da Irin, domin samun damar tattaunawa kan aikin noma na shekarar 2024 a fadin kasar nan.

  • Sanata Yari Ya Samar Da Taki Ga Manoman Zamfara A Kan Naira 20,000
  • Hare-haren Ƴan Bindiga A Jihar Neja Sun Tilasta Wa Manoma Tserewa

Farfesan ya kara da cewa, matsalar da ake samu wajen noma wannan Farin Wake na afkuwa ne sakamakon rashin samun ingantaccen Irin noma.

Ya ci gaba da cewa, a duk shekara a Nijeriya; ana noma Farin Wake kimanin tan miliyan 2.3, duk kuwa da cewa kasar na bukatar wannan Farin Wake sama da tan miliyan 3.

A cewar Lucky, wannan matsala ta rashin samar da isasshen ingantaccen Irin Farin Waken ne ta sa ake shigo da shi daga makwabta kasashen wannan kasa, domin cike gibin da ake da shi.

Ya bayanna cewa, “Ko shakka babu, samar da wannan ingantaccen Irin Farin Wake, zai ba da damar kara yawan nomansa a fadin kasar nan, wanda kuma hakan zai kara samar da dimbin kudaden shiga ga masu nomansa tare da rage yadda ake kashe kudaden”.

Haka zalika, shugaban sashen cibiyar da ke gudanar da aikin cibiyar a Jihar Kano, Dakta Alpha Yaya Kamara a nasa jawabin a wajen taron cewa ya yi, akwai bukatar samar wa da manoma, musamman kananan da ke karkara; ingantaccen Irin Farin Wake.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, shugaban kungiyar masu hada-hadar Irin noma ta kasa, Yusuf Ado Kibiya (SEEDAN) ya bayyana cewa; kungiyar ta yi hadaka da sauran cibiyoyi domin samar da ingantaccen Irin Farin Wake a fadin wannan kasa.

Ya kara da cewa, a shirye kungiyar take; don yin hadaka da sauran masu ruwa da tsaki, domin samar da ingantaccen Irin wannan Iri na Farin Wake.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Arafat: NAHCON Ta Jagoranci Yi Wa Kasa Addu’a

Arafat: NAHCON Ta Jagoranci Yi Wa Kasa Addu'a

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version