Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Sheikh Isyaka Rabi’u Ta Yaye Ɗalibai Sama Da 250

by
5 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Mustapha Ibrahim Kano

Cibiyar Sheikh Muhammadu Rabiu da ke ƙarƙashin shugabancin Khalifa Sheikh Ishaƙa Rabiu Khadimul Ƙur’an shugaban ɗariƙar Tijjaniya ta gama shirin ɗaukar ɗalibai kimanin 3000 wanda za su haddace littafin Allah mai tsarki Al’kurani a wani shiri na Gajeran zango da cibiyar ta ke ɗaukan nauyin gabatarwa duk shekara bayanin hakan ya fito ne daga bakin Alhaji Rabiu ƙarami wanda aka fi sani da IRS a wajen bikin yaye ɗalibai kimanin 250 da suka haddace Al’kurani a wannan cibiya dake ƙarƙashin Khadimul Ƙur’an wanda aka gabatar a wannan lokaci a harabar masallacin Shehu Ibrahim Inyas da ke unguwar Gadon Ƙaya cikin birnin Kano.

Alhaji ƙarami ya ƙara da cewa Khalifa Ishaƙa Rabiu ne ya ke ɗaukar nauyin abincin waɗannan ɗalibai da sauran kayayyakin buƙatu na ɗalibai da cibiyar ke buƙata har zuwa biyan Malamai da sauran su inda ya ce burinmu mu temakawa Khalifa ba dan Khalifa bazai iya ba a’a muna san yin hakan ne domin neman Albarka da kuma neman shiga cikin wannan aiki na alkhairi duniya da lahira.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

Shima a jawabinsa Alhaji Ibrahim Isah wanda aka fi Sa ni da JARIYA babban jami’in karɓar baƙi na Khalifa Ishaƙa Rabiu wanda ya yi magana a madadin Khalifa ya ce ba abun da Khalifa ya fi sha’awa kamar yiwa Al’kurani da makarantansa hidima dan haka kullum burin Khalifa ya ga ya inganta karatun Al’kurani mai girma kuma suna jin daɗi akan yadda Khalifa ke ɗaukar duk wani hadiminsa a matsayin “ɗa ta hanyar riƙe su da amana da haƙuri da kuma gaya musu gaskiya komai ɗacinta ga duk wanda ya yi ba dai dai ba.

Shi kuwa mai baiwa shugaban ƙasa Muhammadu Buhari shawara akan harkar Rediyo da Telebijin Honarabil Sha’aban Sharaɗa ya ce Najeriya na amfana da ga irin addu’oi neman zaman lafiya da ƙaruwar arziƙi da Khalifa da mabiyansa da masoyan ƙasan nan ke yi a koda yaushe dan haka ya ya bawa Khalifa akan wannan aikin alkhairi.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Katsina Ta Yi Gargaɗi Ga Makiyayan Jihar

Next Post

Ba Za A Rage Masu Karɓar Fansho A Jihar Kaduna Ba –Ramalan

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
15 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
17 hours ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
19 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
3 days ago
0

...

Next Post

Ba Za A Rage Masu Karɓar Fansho A Jihar Kaduna Ba –Ramalan

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: