Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Cibiyoyin Da Aka Kama Da Satar Jarrabawar SSCE Sun Fuskanci Tsattsauran Hukunci

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar SSCE Na 2020

by Khalid Idris Doya
January 14, 2021
in LABARAI
1 min read
NECO
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandari ta kasa (NECO) a jiya Laraba ne ta sake sakamakon jarrabawar daliban da suka zana jarrabawa ta kammala sakandare (SSCE) da suka kammala a tsakanin watan Oktoba da Nuwamba, inda hukumar ta dauki tsattsauran mataki kan cibiyoyin da aka kama da satar jarrabawa.

Sakamakon jarabawar ya nuna cewa daga cikin dalibai 1,209,992 da suka zana jarabawar, dalibai 894,101 sun samu nasara da sakamako mai kyau ciki har da darasin Turanci da na Lissafi.

samndaads

Bayanin fitar sakamakon, wanda ya fito ta hannun Rijistara da Babban Jami’imin gudanarwa (CEO) na hukumar NECO, Farfesa Godswill Obioma, ya nuna cewa sun samu kesa-kesan magudin jarabawa guda 33,470, yana mai karawa da cewa makaratun 12 ne wannan lamarin ya shafa tare da samun masu sanya ido 24 cikin lamarin.

Rijistaran ya bayyana cewar makarantun da aka samu da magudin jarabawa, an daina la’akari da su na tsawon shekara biyu, yayin da kuma jami’an sanya ido ‘Sufabaizos’ guda 24 da aka samu da hannu cikin lamarin an dakatar da su bisa samunsu da laifuka daban-daban da suka shafi magudi.

Shugaban ya kuma bayyana cewar sun shirya wani shiri na musamman da zai baiwa daliban da suka gaza samun damar zana jarabawarsu sakamakon zanga-zangar ENDSARS.

Obioma ya jero sunayen jihohin da matsalar jarabawa ya shafa sakamakon matsalar zanga-zangar EndSARS, sun kunshi Oyo, Osun, Ekiti, Legas, Edo, Ondo da kuma wasu cibiyoyin zana jarabawa a jihar Ribas, Abia, Enugu da babban birnin tarayya Abuja.

A cewarsa, daga cikin dalibai 1,221,447 d asuka zana jarabawar, dalibai 665,830 maza ne, a yayin da kuma 555,617 suka kasance mata.

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Zakara Ya Kashe Mutum A Yayin Fadan Zakaru

Next Post

Tilastawa Kamfanoni Noma Zai Rage Tsadar Abinci, Ba Bude Iyakoki Ba – Munkaila Garba

RelatedPosts

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yau Za A Yi Karon Batta A Zaben Kananan Hukumomin Jihar Kano

by Khalid Idris Doya
2 mins ago
0

 Jam’iyyu 11 ne za su fafata PDP Kwankwasiyya ta ce,...

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Khalid Idris Doya
14 mins ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Ali Baba

Zaben Kananan Hukumomi: PDP Kwankwasiyya Ta Maka KASEIC A Kotu

by Khalid Idris Doya
30 mins ago
0

Bangaren Kwankwasiyya na jam'iyyar PDP a jihar Kano, ta jadadda...

Next Post
Munkaila Garba

Tilastawa Kamfanoni Noma Zai Rage Tsadar Abinci, Ba Bude Iyakoki Ba - Munkaila Garba

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version