• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya

by Abubakar Sulaiman
1 month ago
Tsaro

A ƙalla jami’an tsaro 53 aka kashe a faɗin Najeriya cikin makonni biyu da suka gabata, bisa ga ƙididdigar da Daily Trust ta tattara daga rahotannin kafafen watsa labarai. Waɗanda aka kashe sun haɗa da Sojoji, da ƴansanda, da jami’an NSCDC, da na shige-da-fice da na haraji, da kuma na sa-kai, da mambobin JTF da ƙungiyoyin tsaron al’umma na jihohi. Wannan adadi bai haɗa da rahotannin da ba a bayar ba.

Yawancin jami’an an kashe su ne yayin da suke amsa kiran kai hari kan al’umma, yayin da wasu kuma aka yi musu kwanton ɓauna a wuraren binciken ababen hawa da sansanonin tsaro. Manyan hare-haren kwanan nan sun faru ne a jihohin Biniwe da Kogi, inda ƴan bindiga suka hallaka jami’an ƴansanda bakwai da wasu jami’an tsaro a hare-hare dabam-dabam tsakanin Juma’a da Lahadi. Haka kuma an yi garkuwa da wasu jami’an a lamarin da ya auku a Binuwe

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa 9 NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Waɗannan kashe-kashen sun ƙara haskaka yadda barazanar tsaro ke ta ƙara jawo asarar rayukan jami’an tsaro a Nijeriya. Binciken da Daily Trust ta gudanar a watan Disambar 2024 ya nuna cewa an kashe a ƙalla ƴan sanda 229 daga Janairu 2023 zuwa Oktoba 2024 sakamakon hare-haren ƴan bindiga, da na masu tada kayar baya, masu al’ada da kuma ƴan fashi da makami. Sabbin hare-haren sun nuna cewa tashin hankali na ƙaruwa duk da yunƙurin samar da tsaro da ake ci gaba da gudanarwa.

A martanin Hukumar DSS, ta gurfanar da mutane tara a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja a makon jiya kan zargin hannu a kisan da aka yi kwanan nan a jihohin Binuwe da Filato. Cikin waɗanda aka gurfanar har da Haruna Adamu da Muhammad Abdullahi daga Jihar Nasarawa, bisa zargin hannu a kisan gilla da aka yi a Guma LGA ta Benue.

Haka kuma an gurfanar da Terkende Ashuwa da Amos Alede bisa zargin ramuwar gayya da ta haddasa lalata kadarori da rasa shanu 12 a ƙauyen Ukpam. DSS ta kuma gurfanar da wani mutum daban kan mallakar bindigogi M16 guda bakwai ba bisa ƙa’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato

Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.