Cire Tallafi: Gwamnan Gombe Ya Raba Kayayyakin Abinci Da Kayan Noma Ga Mutane 450,000
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafi: Gwamnan Gombe Ya Raba Kayayyakin Abinci Da Kayan Noma Ga Mutane 450,000

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya kaddamar da rabon kayan abinci da kayan noma don rage matsalolin tattalin arziki da ake fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur ga al’ummar jihar. 

 

Da ya ke jawabi a waje bikin rabon kayayyakin wadda aka gudanar a fadar Sarkin Yamaltu da ke Dadinkowa jiya, Gwamnan ya bayyana cewa kaddamar da rabon kayan tallafin wani gagarumin kokari ne na tallafawa fiye da mutane 450,000 da za su ci gajiya a fadin kananan hukumomi 11 na jihar.

  • Lalacewar Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Ta Zama Tarkon Mutuwa Ga Matafiya – Gwamna Inuwa

“A kashi na farko da muka kaddamar a yau, za mu tallafawa mutane dubu 30,000 ne inda kowane mutum zai samu buhun shinkafa mai girman Kilogram biyar da katon din macaroni daya da buhunan taki biyu da lita biyu na maganin kashe kwari”.

 

“Abin da ya sa wannan shiri ya sha bambam da sauran shirye-shirye shi ne dabarar sanya kayan noma a cikin rabon kayan abinci, wannan shawarar tana da matukar tasiri duba da yadda kaso mai tsoka na al’ummar Jihar Gombe sun dogara ne da noma don gudanar da harkokin rayuwarsu.”

Gombe

A cewarsa, ba da tallafin noman zai taimaka matuka wajen samar da isasshen abinci a lokacin kaka.

 

Da yake bayyana wajibcin cire tallafin man fetur, Gwamna Inuwa ya ce hakan wani mataki ne na tabbatar da dorewar tattalin arziki da ci gaba. Ya kara da cewa, an tsara tallafin ne bayan fahimtar irin kalubale daban-daban da magidanta ke fuskanta a Jihar Gombe sakamakon tabarbarewar tattalin arziki.

 

Baya ga rabon kayayyakin, Gwamna Inuwa ya ce, shirin tallafin yana kuma nuna tausayi da jajircewarsa ga jin dadin kowane dan Jihar Gombe.

 

Don haka ya bukaci al’ummar jihar su sanya dabi’un tausayi da hadin kai a cikin mu’amalarsu, tare da tallafawa mabukata.

 

Gwamnan ya yi kira ga jami’an rabon kayayyakin da ‘yan sa kai su gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da rikon amana don tabbatar da gaskiya da adalci.

Gombe

Gwamna Inuwa Yahaya ya tabbatarwa jama’a cewa gwamnatin sa tana kokarin ƙara samar da ayyukan yi ga al’umma don bunkasar harkokin ci gaba, da dakile kalubalen tattalin arzikin da jama’a ke fuskanta.

 

Shugaban kwamitin kula da rabon kayan abinci na jiha Abdullahi Haruna Abdullahi, ya tabbatarwa Gwamnan cewa kwamitin zai gudanar da aikinsa cikin tsantseni da tsoron Allah don amfanar al’umma.

 

Abdullahi wanda kuma shi ne Sakataren zartarwa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Gombe SEMA, ya bayyana cewa an kafa wasu kananan kwamitoci a matakin kananan hukumomi da gundumomi don tabbatar da cewa kayayyakin sun kai ga marasa galihu a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Next Post
Xi Jinping Zai Halarci Taron Ganawar Shugabannin Kasashen BRICS Karo Na 15

Xi Jinping Zai Halarci Taron Ganawar Shugabannin Kasashen BRICS Karo Na 15

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version