Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

bySulaiman
2 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Ƙungiyar ‘Yan Kasuwar Man Fetur Masu Zaman Kansu (IPMAN) bisa namijin ƙoƙarin da suke yi na ganin an fito da tsarin samar da makamashi na wanda Ba man fetur ba da Gwamnatin Tarayya ta ɓullo da shi bayan cire tallafin man fetur da Shugaba Bola Tinubu ya yi.

Idris, wanda ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓi baƙuncin kwamitin gudanarwa na IPMAN na ƙasa a ofishinsa da ke Abuja a ranar Alhamis don ziyarar ban-girma, ya ce Gwamnatin Tarayya na da burin rage farashin sufuri da sama da kashi 50 cikin ɗari ta hanyar shirin amfani da motoci masu aiki da iskar gas (CNG Initiative).

  • Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Kai Don Ciyar Da Jihar Gaba
  • ‘Yan Sandan Sin Sun Kama Tan 25.9 Na Miyagun Kwayoyi A Shekarar 2023

“Bayan cire tallafin man fetur, ba shakka ana tsammanin farashin man fetur zai hauhawa. Hakan kuma zai shafi farashin sufurin da ‘yan Nijeriya ke kaiwa da komowa a wuraren ayyukansu daban-daban.

“Nan da nan Gwamnatin Tarayya ta yi tunanin cewa ya kamata, ban da wasu matakan, ta ɓullo da CNG. Ana sa ran CNG zai rage farashin sufuri da sama da kashi 50 cikin ɗari, kuma ina farin cikin cewa IPMAN na kan gaba wajen ganin an cimma nasarar shirin CNG ɗin,” inji shi.

Ministan ya ce matakin da Shugaba Tinubu ya ɗauka na cire tallafin man fetur ya ba da dama ta musamman ga ƙungiyoyi irin su IPMAN da za su kasance kan gaba wajen tsara yanayin makamashi a Nijeriya.

Ministan ya ce Nijeriya a matsayinta na ƙasa ta na neman wasu hanyoyin da za ta rage farashin sufuri kuma CNG ita ce hanya mafi inganci da za a bi.

Idris ya ce tuni Gwamnatin Tarayya a matakin farko ta ware naira biliyan 100 domin sayen motocin bas ɗin CNG da kuma kafa cibiyoyin CNG a faɗin ƙasar nan.

Ya ce wannan yana baya ga ɓullo da dokar hana biyan haraji ga masu shigo da kaya na CNG da sauran masu saka hannun jari a wannan ɓangaren.

“Za ku iya tunawa Gwamnatin Tarayya tun farko ta ware naira biliyan 100 don sayen motocin bas na CNG da kuma kafa cibiyoyin CNG a faɗin kasar nan,” inji shi.

Yayin da yake neman goyon bayan ƙungiyar IPMAN ɗin domin samun nasarar shirin Sabuwar Fata na Shugaba Tinubu, ministan ya yi masu godiya bisa la’akari da ma’aikatarsa da ma hukumominta a matsayin amintattun abokan hulɗar su na ƙoƙarin daƙile labaran ƙarya da ake yaɗawa kan ayyukan IPMAN.

Ministan ya koka da yadda labaran ƙarya ke yin illa ga ɓangarori daban-daban na al’umma, ya kuma ce akwai fatan alheri ta hanyar haɗin gwiwar ma’aikatarsa da UNESCO na samar da matakan daƙile illolin labaran ƙarya.

Ya yi alƙawarin ba da ƙarin haske ga shirin cikin gida na ƙungiyar mai taken “IPMAN A Yau”, a kan hukumomin yaɗa labarai daban-daban da ke ƙarƙashin ma’aikatarsa.

Idris ya kuma yi alƙawarin yin amfani da tsarin mambobi 30,000 na IPMAN wajen aiwatar da shirye-shiryen sake daidaita darajar da ke ƙunshe a cikin Yarjejeniyar Ƙimar Kasa.

A nasa jawabin, shugaban ƙungiyar IPMAN, Alhaji Abubakar Maigandi Shettima, ya yi alƙawarin ba da goyon baya ga Shirin CNG na shugaban ƙasa, kuma ya yi alƙawarin bai wa gwamnati haɗin kai a cikin shirin samar da makamashin da ba fetur ba, wanda zai ba da ƙwarin gwiwa wajen tabbatar da ajandar Sabuwar Fata ta shugaban ƙasa.

Ya koka kan yadda a kullum ake sarrafa farashin man fetur ta hanyar yaɗa labaran ƙarya tare da neman goyon bayan ma’aikatar domin yaƙar wannan barazana.

Shettima ya ce a nasu ɓangaren, IPMAN ta fito da wani shiri mai taken “IPMAN A Yau” – shirin rediyo da talabijin, wanda zai zama tushen labarai na gaskiya kan ayyukan ƙungiyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Next Post
Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

Kamfanonin Ketare Dake Kasar Sin Sun Amince Da Makomar Tattalin Arzikinta

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version