Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

COVID-19: Annoba Ta Lamuke Amurkawa Sama Da Rabin Miliyan

by
1 year ago
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
COVID-19: Annoba Ta Lamuke Amurkawa Sama Da Rabin Miliyan
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Ahmad Fagam

Da alama dai har yanzu ba ta sauya zani ba, domin kuwa Amurka ce kasar da ta fi kowace kasa a duniya fuskantar bala’in shu’umar cutar shakewar numfashi ta COVID-19.

A bisa ga alkaluman da cibiyar nazarin kimiyya da fasaha ta jami’ar Johns Hopkins ta fitar a karshen makon jiya ya nuna cewa, Amurkar ita ce ke jagorantar duniya ta fuskar adadin mutanen da annobar ta kashe da kuma wadanda suka kamu da cutar mashako ta COVID-19.

Labarai Masu Nasaba

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

Kididdigar baya bayan nan ta nuna cewa, ya zuwa ranar Asabar din da ta gabata adadin mutanen da annobar COVID-19 ta hallaka a fadin duniya ya zarce miliyan 3. Ya zuwa ranar Asabar din jimillar mutanen da cutar ta kashe a duniya ya kai 3,001,892, yayin da adadin mutanen da suka kamu da cutar a fadin duniya ya zarce miliyan 140. Cibiyar nazarin kimiyya da fasahar ta tabbatar da cewa Amurka ce kasar da annobar ta fi yi wa mummunar illa, yayin da kasar ke da yawan mutanen da suka kamu da cutar COVID-19 kimanin 31,567,744, kana cutar ta hallaka Amurkawa 566,240, wato sama da kashi 22 bisa 100 na yawan mutanen da suka kamu da cutar a fadin duniya, sannan sama da kashi 18 bisa 100 na yawan mutanen da cutar ta kashe a duniya. Kasashen da suka rasa rayukan al’ummarsu wanda adadin ya zarce 100,000, sun hada da India, Birtaniya, Italiya, Rasha da Faransa. A ranar 28 ga watan Satumbar 2020, adadin mutanen da cutar COVID-19 ta kashe a duniya ya cika miliyan 1, sannan cutar ta hallaka mutane miliyan 2 ya zuwa ranar 15 ga watan Janairun shekarar nan ta 2021. Koda yake, dama dai tun a farkon barkewar annobar ta COVID-19 a karshen Disambar shekarar 2019 masana sun sha yiwa gwamnatin Amurka gargadi cewa rashin daukar kwararan matakan da suka dace a kan lokaci ka iya ta’azzara al’amurra game da bazuwar cutar muddin aka gaza daukar matakai mafiya dacewa. Koda a cikin wannan mako sai da mai ba da shawara ga hukumar yaki da cutuka masu yaduwa ta Amurka Dr Antony Fauci, ya yi barazanar cewa har yanzu Amurkar tana cikin halin rashin tabbas kuma mai yiwuwa ne kasar za ta ci gaba da fuskantar hadarin hasarar dubban rayukan ’yan kasar nan da wasu watanni masu zuwa a sanadiyyar cutar ta COVID-19. (Ahmad Fagam)

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Ya Kamata Kasar Amurka Ta Koyi Fasahar Yin Takara Bisa Wani Nagartaccen Yanayi

Next Post

Don Me Kasashen Duniya Suka Kara Maida Hankali Kan Dandalin Tattaunawa Na Kasashen Asiya A Bo’ao?

Labarai Masu Nasaba

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

by CMG Hausa
13 hours ago
0

...

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

by CMG Hausa
14 hours ago
0

...

Al’ummar Afirka Ba Su Bukatar A Yi Musu Lacca

Al’ummar Afirka Ba Su Bukatar A Yi Musu Lacca

by CMG Hausa
16 hours ago
0

...

Masana sun yi Allah wadai da yunkurin Amurka na neman dakile cigaban al’ummar Xinjiang

Masana sun yi Allah wadai da yunkurin Amurka na neman dakile cigaban al’ummar Xinjiang

by CMG Hausa
16 hours ago
0

...

Next Post
Don Me Kasashen Duniya Suka Kara Maida Hankali Kan Dandalin Tattaunawa Na Kasashen Asiya A Bo’ao?

Don Me Kasashen Duniya Suka Kara Maida Hankali Kan Dandalin Tattaunawa Na Kasashen Asiya A Bo’ao?

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: